1 Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2 “Yaushe za ka gama maganganun nan?
3 Don me muke kamar shanu a wurinka,
4 Kai da ka yayyage kanka don haushi,
5 “An kashe fitilar mugu;
6 Wutar cikin tentinsa ta zama duhu;
7 Ƙarfin takawarsa ya ragu;
8 Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga,
9 Tarko ya kama ɗiɗɗigensa;
10 An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa;
11 Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe
12 Masifa tana jiransa;
13 Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa;
14 An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa
15 Wuta ta cinye tentinsa;
16 Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa
17 An manta da shi a duniya;
18 An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu,
19 Ba shi da ’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa,
20 Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi;
21 Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake,