Números 33
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVI
1 Ga wuraren da Isra’ilawa suka yi sansani sa’ad da suka fito runduna-runduna a ƙarƙashin Musa da Haruna daga Masar.
1 Estas são as jornadas dos israelitas quando saíram do Egito, organizados segundo as suas divisões, sob a liderança de Moisés e Arão.
2 Bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya rubuta wuraren tafiye-tafiyensu da sansaninsu. Ga yadda tafiye-tafiyen suka kasance.
2 Por ordem do Senhor Moisés registrou as etapas da jornada deles. Esta foi a jornada deles, por etapas:
3 Isra’ilawa sun tashi daga Rameses a rana ta goma sha biyar, ga watan fari, kashegarin Bikin Ƙetarewa. Suka fita gabagadi a gaban dukan Masarawa,
3 Os israelitas partiram de Ramessés no décimo quinto dia do primeiro mês, no dia seguinte ao da Páscoa. Saíram, marchando desafiadoramente à vista de todos os egípcios,
4 waɗanda suke binne gawawwakin ’ya’yan farinsu da Ubangiji ya karkashe; gama Ubangiji ya hukunta allolinsu.
4 enquanto estes sepultavam o primeiro filho de cada um deles, que o Senhor matou. O Senhor impôs castigo aos seus deuses.
5 Isra’ilawa suka tashi daga Rameses, suka yi sansani a Sukkot.
5 Os israelitas partiram de Ramessés e acamparam em Sucote.
6 Suka tashi daga Sukkot, suka yi sansani a Etam, a gefen hamada.
6 Partiram de Sucote e acamparam em Etã, nos limites do deserto.
7 Suka tashi daga Etam, suka koma baya zuwa Fi Hahirot, wajen gabashin Ba’al-Zafon, suka yi sansani kusa da Migdol.
7 Partiram de Etã, voltaram para Pi-Hairote, a leste de Baal-Zefom, e acamparam perto de Migdol.
8 Suka tashi daga Fi Hahirot, suka ratsa cikin teku zuwa hamada, bayan sun yi tafiya kwana uku a cikin Hamadan Etam, sai suka yi sansani a Mara.
8 Partiram de Pi-Hairote e atravessaram o mar chegando ao deserto, e, depois de viajarem três dias no deserto de Etã, acamparam em Mara.
9 Suka tashi daga Mara, suka tafi Elim, inda akwai maɓulɓulan ruwa goma sha biyu, da itatuwan dabino guda saba’in, suka yi sansani a can.
9 Partiram de Mara e foram para Elim, onde havia doze fontes e setenta palmeiras, e acamparam ali.
10 Suka tashi daga Elim, suka yi sansani kusa da Jan Teku.
10 Partiram de Elim e acamparam junto ao mar Vermelho.
11 Suka tashi daga Jan Teku, suka yi sansani a Hamadan Sin.
11 Partiram do mar Vermelho e acamparam no deserto de Sim.
12 Suka tashi daga Hamadan Sin, suka yi sansani a Dofka.
12 Partiram do deserto de Sim e acamparam em Dofca.
13 Suka tashi daga Dofka, suka yi sansani a Alush.
13 Partiram de Dofca e acamparam em Alus.
14 Suka tashi daga Alush, suka yi sansani a Refidim, inda babu ruwan da mutane za su sha.
14 Partiram de Alus e acamparam em Refidim, onde não havia água para o povo beber.
15 Suka tashi daga Refidim, suka yi sansani a Hamadan Sinai.
15 Partiram de Refidim e acamparam no deserto do Sinai.
16 Suka tashi daga Hamadan Sinai, suka yi sansani a Kibrot Hatta’awa.
16 Partiram do deserto do Sinai e acamparam em Quibrote-Hataavá.
17 Suka tashi daga Kibrot Hatta’awa, suka yi sansani a Hazerot.
17 Partiram de Quibrote-Hataavá e acamparam em Hazerote.
18 Suka tashi daga Hazerot, suka yi sansani a Ritma.
18 Partiram de Hazerote e acamparam em Ritmá.
19 Suka tashi daga Ritma, suka yi sansani a Rimmon Ferez.
19 Partiram de Ritmá e acamparam em Rimom-Perez.
20 Suka tashi daga Rimmon Ferez, suka yi sansani a Libna.
20 Partiram de Rimom-Perez e acamparam em Libna.
21 Suka tashi daga Libna, suka yi sansani a Rissa.
21 Partiram de Libna e acamparam em Rissa.
22 Suka tashi daga Rissa, suka yi sansani a Kehelata.
22 Partiram de Rissa e acamparam em Queelata.
23 Suka tashi daga Kehelata, suka yi sansani a Dutsen Shefer.
23 Partiram de Queelata e acamparam no monte Séfer.
24 Suka tashi daga Dutsen Shefer, suka yi sansani a Harada.
24 Partiram do monte Séfer e acamparam em Harada.
25 Suka tashi daga Harada, suka yi sansani a Makhelot.
25 Partiram de Harada e acamparam em Maquelote.
26 Suka tashi daga Makhelot, suka yi sansani a Tahat.
26 Partiram de Maquelote e acamparam em Taate.
27 Suka tashi daga Tahat, suka yi sansani a Tera.
27 Partiram de Taate e acamparam em Terá.
28 Suka tashi daga Tera, suka yi sansani a Mitka.
28 Partiram de Terá e acamparam em Mitca.
29 Suka tashi daga Mitka, suka yi sansani a Hashmona.
29 Partiram de Mitca e acamparam em Hasmona.
30 Suka tashi daga Hashmona, suka yi sansani a Moserot.
30 Partiram de Hasmona e acamparam em Moserote.
31 Suka tashi daga Moserot, suka yi sansani a Bene Ya’akan.
31 Partiram de Moserote e acamparam em Benê-Jaacã.
32 Suka tashi daga Bene Ya’akan, suka yi sansani a Hor Haggidgad.
32 Partiram de Benê-Jaacã e acamparam em Hor-Gidgade.
33 Suka tashi daga Hor Haggidgad, suka yi sansani a Yotbata.
33 Partiram de Hor-Gidgade e acamparam em Jotbatá.
34 Suka tashi daga Yotbata, suka yi sansani a Abrona.
34 Partiram de Jotbatá e acamparam em Abrona.
35 Suka tashi daga Abrona, suka yi sansani a Eziyon Geber.
35 Partiram de Abrona e acamparam em Eziom-Geber.
36 Suka tashi daga Eziyon Geber, suka yi sansani a Kadesh, cikin Hamadan Zin.
36 Partiram de Eziom-Geber e acamparam em Cades, no deserto de Zim.
37 Suka tashi daga Kadesh, suka yi sansani a Dutsen Hor, a iyakar Edom.
37 Partiram de Cades e acamparam no monte Hor, na fronteira de Edom.
38 Bisa ga umarni Ubangiji, Haruna firist, ya hau Dutsen Hor, inda ya mutu a rana ta fari ga watan biyar, a shekara ta arba’in, bayan Isra’ilawa suka fito daga Masar.
38 Por ordem do Senhor, o sacerdote Arão subiu o monte Hor, onde morreu no dia primeiro do quinto mês do quadragésimo ano depois que os israelitas saíram do Egito.
39 Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku, sa’ad da ya mutu a Dutsen Hor.
39 Arão tinha cento e vinte e três anos de idade quando morreu no monte Hor.
40 Sarki Arad Bakan’ane, wanda yake zaune a Negeb na Kan’ana, ya ji labari cewa Isra’ilawa suna zuwa.
40 O rei cananeu de Arade, que vivia no Neguebe, na terra de Canaã, soube que os israelitas estavam chegando.
41 Suka tashi daga Dutsen Hor, suka yi sansani a Zalmona.
41 Eles partiram do monte Hor e acamparam em Zalmona.
42 Suka tashi daga Zalmona, suka yi sansani a Funon.
42 Partiram de Zalmona e acamparam em Punom.
43 Suka tashi daga Funon, suka yi sansani a Obot.
43 Partiram de Punom e acamparam em Obote.
44 Suka tashi daga Obot, suka yi sansani a Iye Abarim, a iyakar Mowab.
44 Partiram de Obote e acamparam em Ijé-Abarim, na fronteira de Moabe.
45 Suka tashi daga Iyim, suka yi sansani a Dibon Gad.
45 Partiram de Ijim e acamparam em Dibom-Gade.
46 Suka tashi daga Dibon Gad, suka yi sansani a Almon Dibilatayim.
46 Partiram de Dibom-Gade e acamparam em Almom-Diblataim.
47 Suka tashi daga Almon Dibilatayim, suka yi sansani a duwatsun Abarim, kusa da Nebo.
47 Partiram de Almom-Diblataim e acamparam nos montes de Abarim, defronte de Nebo.
48 Suka tashi daga duwatsun Abarim, suka yi sansani a filayen Mowab kusa da Urdun, ɗaura da Yeriko.
48 Partiram dos montes de Abarim e acamparam nas campinas de Moabe junto ao Jordão, do outro lado de Jericó.
49 A can filayen Mowab, suka yi sansani kusa da Urdun ɗaura da Bet-Yeshimot har zuwa Abel-Shittim.
49 Nas campinas de Moabe eles acamparam junto ao Jordão, desde Bete-Jesimote até Abel-Sitim.
50 A filayen Mowab kusa da Urdun ɗaura da Yeriko ne Ubangiji ya ce wa Musa,
50 Nas campinas de Moabe, junto ao Jordão, do outro lado de Jericó, o Senhor disse a Moisés:
51 “Ka gaya wa Isra’ilawa cewa, ‘Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa Kan’ana,
51 "Diga aos israelitas: Quando vocês atravessarem o Jordão para entrar em Canaã,
52 ku kori dukan mazaunan ƙasar a gabanku. Ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsu, da siffofinsu na zubi, ku kuma rurrushe dukan masujadansu na kan tudu.
52 expulsem da frente de vocês todos os habitantes da terra. Destruam todas as imagens esculpidas e todos os ídolos fundidos, e derrubem todos os altares idólatras deles.
53 Ku mallaki ƙasar, ku kuma zauna a ciki, gama na ba ku ƙasar, ku mallake ta.
53 Apoderem-se da terra e instalem-se nela, pois eu lhes dei a terra para que dela tomem posse.
54 Ku rarraba ƙasar ta wurin jefan ƙuri’a, bisa ga kabilanku. Kabilar da take babba, a ba ta babban gādo, ƙarami kabila kuwa, a ba ta ƙaramin gādo. Duk abin da ƙuri’a ta ba su, shi zai zama nasu. Ku rarraba wannan bisa zuriyar kakanninku.
54 Distribuam a terra por sorteio, de acordo com os seus clãs. Aos clãs vocês darão uma herança maior, e aos menores, uma herança menor. Cada clã receberá a terra que lhe cair por sorte. Distribuam-na entre as tribos dos seus antepassados.
55 “ ‘Amma in ba ku kori mazaunan ƙasar ba, waɗanda kuka bari su ci gaba da zama, za su zama muku hakki a idanunku, da kuma ƙayayyuwa a bayanku. Za su ba ku wahala a ƙasar da kuke zama.
55 "Se, contudo, vocês não expulsarem os habitantes da terra, aqueles que vocês permitirem ficar se tornarão farpas em seus olhos e espinhos em suas costas. Eles lhes causarão problemas na terra em que vocês irão morar.
56 Sa’an nan kuwa zan yi muku abin da na shirya yin musu.’ ”
56 Então farei a vocês o mesmo que planejo fazer a eles".
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Números 33, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.