Mateus 22

Litafi Mai-tsarki (HAU_ULB) vs NAA

Sair da comparação
NAA Nova Almeida Atualizada 2017
1 Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
1 De novo Jesus lhes falou por parábolas, dizendo:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
2 — O Reino dos Céus é semelhante a um rei que preparou uma festa de casamento para seu filho.
3 Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
3 Enviou os seus servos a chamar os convidados para a festa, mas estes não quiseram vir.
4 Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
4 Enviou ainda outros servos, dizendo: “Digam aos convidados: Eis que já preparei o meu banquete; os meus bois e animais da engorda já foram abatidos, e tudo está pronto; venham para a festa.”
5 Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
5 Mas os convidados não se importaram e se foram, um para o seu campo, outro para o seu negócio.
6 Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
6 Outros, agarrando os servos, os maltrataram e mataram.
7 Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
7 — O rei ficou furioso e, enviando as suas tropas, exterminou aqueles assassinos e incendiou a cidade deles.
8 Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
8 Então disse aos seus servos: “A festa está pronta, mas os convidados não eram dignos.
9 Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
9 Vão, pois, para as encruzilhadas dos caminhos e convidem para o banquete todos os que vocês encontrarem.”
10 Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
10 E, saindo aqueles servos pelas estradas, reuniram todos os que encontraram, maus e bons; e a sala do banquete ficou cheia de convidados.
11 Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
11 — Mas, quando o rei entrou para ver os que estavam à mesa, notou ali um homem que não trazia veste nupcial
12 Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
12 e perguntou-lhe: “Amigo, como você entrou aqui sem veste nupcial?” E ele emudeceu.
13 Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
13 Então o rei ordenou aos serventes: “Amarrem os pés e as mãos dele e atirem-no para fora, nas trevas; ali haverá choro e ranger de dentes.”
14 Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
14 Porque muitos são chamados, mas poucos são escolhidos.
15 Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
15 Então os fariseus se retiraram e consultaram entre si como surpreenderiam Jesus em alguma palavra.
16 Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
16 E enviaram-lhe discípulos, juntamente com os herodianos, para lhe dizer: — Mestre, sabemos que o senhor é verdadeiro e que ensina o caminho de Deus de acordo com a verdade, sem se importar com a opinião dos outros, porque não olha para a aparência das pessoas.
17 To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
17 Assim sendo, diga-nos o que o senhor acha: é lícito pagar imposto a César ou não?
18 Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
18 Mas Jesus, percebendo a maldade deles, respondeu:
19 Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
19 Mostrem-me a moeda do imposto. Trouxeram-lhe um denário.
20 Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
20 E Jesus lhes perguntou:
21 Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
21 Eles responderam: — De César. Então Jesus lhes disse:
22 Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
22 Ouvindo isto, se admiraram e, deixando-o, foram embora.
23 A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
23 Naquele dia, alguns saduceus, que dizem não haver ressurreição, aproximaram-se de Jesus e lhe perguntaram:
24 cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
24 — Mestre, Moisés disse: “Se alguém morrer, não tendo filhos, o irmão desse homem deve casar com a viúva e gerar descendentes para o falecido.”
25 Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
25 Ora, havia entre nós sete irmãos. O primeiro, tendo casado, morreu e, não tendo descendência, deixou sua mulher para seu irmão.
26 Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
26 O mesmo aconteceu com o segundo, com o terceiro, até o sétimo.
27 Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
27 Por fim, depois de todos, morreu também a mulher.
28 To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
28 Portanto, na ressurreição, de qual dos sete ela será esposa? Porque todos casaram com ela.
29 Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
29 Jesus respondeu:
30 Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
30 Porque, na ressurreição, nem casam, nem se dão em casamento, mas são como os anjos no céu.
31 Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
31 Quanto à ressurreição dos mortos, vocês nunca leram o que Deus disse a vocês:
32 'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
32 “Eu sou o Deus de Abraão, o Deus de Isaque e o Deus de Jacó”? Ele não é Deus de mortos, e sim de vivos.
33 Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 Ouvindo isto, as multidões se maravilhavam da sua doutrina.
34 Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
34 Entretanto, os fariseus, sabendo que Jesus havia silenciado os saduceus, reuniram-se em conselho.
35 Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
35 E um deles, intérprete da Lei, querendo pôr Jesus à prova, perguntou-lhe:
36 “Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
36 — Mestre, qual é o grande mandamento na Lei?
37 Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
37 Jesus respondeu:
38 Wannan itace babbar doka ta farko.
38 Este é o grande e primeiro mandamento.
39 Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
39 E o segundo, semelhante a este, é: “Ame o seu próximo como você ama a si mesmo.”
40 Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
40 Destes dois mandamentos dependem toda a Lei e os Profetas.
41 Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
41 Estando reunidos os fariseus, Jesus lhes perguntou:
42 Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
42 — O que vocês pensam do Cristo? De quem é filho? Eles responderam: — De Davi.
43 Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
43 E Jesus perguntou:
44 “Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
44 “Disse o Senhor ao meu Senhor:
45 Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
45 — Portanto, se Davi o chama de Senhor, como ele pode ser filho de Davi?
46 Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.
46 E ninguém podia lhe responder uma palavra; e a partir daquele dia ninguém mais ousou fazer perguntas.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.