Mateus 22

Litafi Mai-tsarki (HAU_ULB) vs ARIB

Sair da comparação
ARIB Almeida Revisada Imprensa Bíblica
1 Yesu ya sake yi masu magana da misalai, yace,
1 Então Jesus tornou a falar-lhes por parábolas, dizendo:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya wa dansa liyafar aure.
2 O reino dos céus é semelhante a um rei, que celebrou as bodas de seu filho.
3 Ya aiki bayinsa su kira wadanda aka gayyata su zo liyafar auren, amma suka ki zuwa.
3 Enviou os seus servos a chamar os convidados para a festa, e estes não quiseram vir.
4 Sai sarkin ya sake aiken wasu bayin, yace, “Ku gaya wa wadanda aka gayyata, “Duba, na shirya liyafata. An yanka bajimaina da kosassun 'yanmarukana, an gama shirya komai. Ku zo wurin bikin auren.”
4 Enviou ainda outros servos com este recado: Dizei aos convidados: Tenho já preparado o meu banquete; as minhas reses e os meus cevados estão mortos, e tudo está pronto; vinde às bodas.
5 Amma mutanen ba su dauki sakon da mahimmanci ba kuma suka yi tafiyarsu. Wani ga gonarsa, wani ga kasuwancinsa.
5 Mas eles não fizeram caso e foram, um para o seu campo, outro para o seu negócio;
6 Sauran kuma suka kama bayin sarkin, suka wulakanta su, suka kuma kashe su.
6 e os outros, agarrando os servos, os ultrajaram e mataram.
7 Amma sarkin ya ji haushi. Ya aika sojojinsa, ku kashe masu kisan kan nan, ku kuma kone birnin su.
7 Irou-se o rei, e mandou as suas tropas exterminar aqueles assassinos e incendiar a sua cidade.
8 Sai ya ce wa bayinsa, 'An gama shirya bikin, amma wadanda aka gayyata ba su cancanta ba.
8 Então disse aos servos: As bodas estão preparadas, mas os convidados não eram dignos;
9 Saboda haka ku je bakin hanya ku gayyaci iyakar yawan mutanen da za ku samu zuwa bukin auren.'
9 ide, pois, às encruzilhadas dos caminhos e chamai para as bodas a quantos encontrardes.
10 Bayin suka tafi hanya suka tattaro dukan mutanen da suka samu, da masu kyau da marassa kyau. Zauren auren kuwa ya cika makil da baki.
10 Indo aqueles servos pelos caminhos, reuniram todos os que encontraram, maus e bons; e a sala nupcial ficou cheia de convivas.
11 Amma da sarkin ya zo don ya ga bakin, sai ya ga wani wanda bai sa kayan aure ba.
11 Mas entrando o rei para ver os convivas, notou ali um homem que não trajava veste nupcial,
12 Sai sarkin ya ce masa, 'Aboki, ta yaya ka shigo nan ba tare da kayan aure ba?' Mutumin kuwa ya rasa ta cewa.
12 e perguntou-lhe: Amigo, como entraste aqui sem veste nupcial? Ele, porém, emudeceu.
13 Sai sarkin ya ce wa bayinsa, 'Ku daure mutumin nan hannu da kafa, ku jefa shi cikin duhun, inda za ayi kuka da cizon hakora.'
13 Então o rei disse aos servos: Atai-o de pés e mãos, e lançai-o nas trevas exteriores; ali haverá o choro e o ranger de dentes.
14 Gama mutane dayawa aka kira, amma kadan aka zaba.”'
14 Pois muitos são chamados, mas poucos escolhidos.
15 Sai Farisawan suka tafi suka shirya makirci akan yadda zasu kama shi ta maganarsa.
15 Então os fariseus se retiraram e consultaram entre si como o apanhariam em alguma palavra;
16 Suka tura masa almajiransu, da Hirudiyawa. Suka ce ma Yesu, “Mallam, mun san kai mai gaskiya ne, kuma kana koyar da hanyar Ubangiji da gaskiya. Ba ka damu da ra'ayin kowa ba, kuma ba ka nuna bambanci a tsakanin mutane.
16 Enviaram os seus discípulos, juntamente com os herodianos, a perguntar: Mestre, sabemos que és verdadeiro e que ensinas o caminho de Deus segundo a verdade, e não se te dá de ninguém, porque não te deixas levar de respeitos humanos;
17 To gaya mana, menene tunaninka? Ya halarta a biya haraji ga Kaisar ko a'a?”
17 dize-nos, pois, qual é o teu parecer; é lícito ou não pagar o tributo a César?
18 Amma Yesu ya gane muguntarsu yace, “Don me kuke gwada ni, ku munafukai?
18 Porém Jesus, tendo percebido a malícia deles, respondeu-lhes: Por que me experimentais, hipócritas?
19 Ku nuna mani sulen harajin.” Sai suka kawo masa sulen.
19 Mostrai-me uma moeda de tributo. Trouxeram-lhe um denário.
20 Yesu yace masu, “Hoto da sunan wanene wadannan?”
20 Ele perguntou: De quem é esta efígie e inscrição?
21 Suka ce masa, “Na Kaisar.” Sai Yesu ya ce masu, “To ku ba Kaisar abubuwan dake na Kaisar, Allah kuma abubuwan dake na Allah.”
21 Responderam: De César. Então lhes disse Jesus: Dai, pois, a César o que é de César, e a Deus o que é de Deus.
22 Da suka ji haka, suka yi mamaki. Sai suka bar shi suka tafi.
22 Ao ouvirem isto, admiraram-se e, deixando-o, foram-se.
23 A ran nan sai wadansu Sadukiyawa, wadanda suka ce ba tashin matattu, suka zo wurinsa. Suka tambaye shi,
23 No mesmo dia vieram alguns saduceus, que dizem não haver ressurreição, e o interrogaram, dizendo:
24 cewa, “Mallam, Musa yace, 'Idan mutum ya mutu, bashi da 'ya'ya, dole dan'uwansa ya auri matarsa ya kuwa haifawa dan'uwansa 'ya'ya.
24 Mestre, Moisés disse: Se alguém morrer sem deixar filhos, seu irmão casará com a viúva e dará sucessão ao falecido.
25 Akwai wasu 'yan'uwa bakwai. Na farkon yayi aure sai ya mutu. Da shike bai bar 'ya'ya ba. Ya bar wa dan'uwansa matarsa.
25 Ora havia entre nós sete irmãos: o primeiro, depois de ter casado, morreu e, não havendo sucessão, deixou sua mulher a seu irmão;
26 Sai dan'uwansa na biyu shi ma yayi haka, haka kuma na ukun, har zuwa dan'uwan na bakwai.
26 do mesmo modo também o segundo e o terceiro, até o sétimo.
27 Bayan dukansu, sai matar ta mutu.
27 Depois de todos eles morreu a mulher.
28 To a tashin matattu, matar wa zata zama a cikin su bakwai din? Don duk sun aure ta.”
28 Na ressurreição, pois, a qual dos sete pertencerá a mulher? porque todos foram casados com ela.
29 Amma Yesu ya amsa yace masu, “Kun bata, domin ba ku san litattafai ko ikon Allah ba.
29 Respondeu-lhes Jesus: Errais, não sabendo as Escrituras, nem o poder de Deus.
30 Domin a tashin matattu basu aure, ba kuma a bada su aure. Maimaikon haka, suna kama da mala'ikun sama.
30 Pois na ressurreição nem os homens casam, nem as mulheres são dadas em casamento porém são como os anjos no céu.
31 Amma game da tashin matattu, ba ku karanta abinda Allah ya fada maku ba, cewa,
31 E, quanto à ressurreição dos mortos, não lestes o que foi dito por Deus:
32 'Nine Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku, da Allah na Yakubu'? Allah ba Allah na matattu bane, amma na rayayyu.”
32 Eu sou o Deus de Abraão, o Deus de Isaque, e o Deus de Jacó? Ora, ele não é Deus de mortos, mas de vivos.
33 Da taron suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 E as multidões, ouvindo isso, se maravilhavam da sua doutrina.
34 Amma da Farisawan suka ji cewa Yesu ya kure Sadukiyawa, sai suka tattara kansu.
34 Os fariseus, quando souberam, que ele fizera emudecer os saduceus, reuniram-se todos;
35 Daya daga cikinsu, masanin shari'a, yayi masa tambaya, yana gwada shi-
35 e um deles, doutor da lei, para o experimentar, interrogou-o, dizendo:
36 “Mallam, wace doka ce mafi girma a cikin shari'a?”
36 Mestre, qual é o grande mandamento na lei?
37 Yesu yace masa, “Ka kaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka.'
37 Respondeu-lhe Jesus: Amarás ao Senhor teu Deus de todo o teu coração, de toda a tua alma, e de todo o teu entendimento.
38 Wannan itace babbar doka ta farko.
38 Este é o grande e primeiro mandamento.
39 Doka ta biyu kuma kamar ta take- 'Ka kaunaci makwabcinka kamar kanka.'
39 E o segundo, semelhante a este, é: Amarás ao teu próximo como a ti mesmo.
40 Akan wadannan dokoki ne dukkan shari'a da annabawa suka rataya.”
40 Destes dois mandamentos dependem toda a lei e os profetas.
41 Yayin da Farisawa suke tattare wuri daya, Yesu yayi masu tambaya.
41 Ora, enquanto os fariseus estavam reunidos, interrogou-os Jesus, dizendo:
42 Yace, “Me kuke tunani game da Almasihu? Shi dan wanene?” Suka ce masa, ''Dan Dauda ne.”
42 Que pensais vós do Cristo? De quem é filho? Responderam-lhe: De Davi.
43 Yesu yace masu, “To ta yaya kuma Dauda cikin Ruhu ya kira shi Ubangiji, yana cewa,
43 Replicou-lhes ele: Como é então que Davi, no Espírito, lhe chama Senhor, dizendo:
44 “Ubangiji ya cewa wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na mai da makiyanka matakin sawayenka.”
44 Disse o Senhor ao meu Senhor: Assenta-te à minha direita, até que eu ponha os teus inimigos de baixo dos teus pés?
45 Idan Dauda ya kira Almasihu 'Ubangiji,' ta yaya ya zama dan Dauda?”
45 Se Davi, pois, lhe chama Senhor, como é ele seu filho?
46 Ba wanda ya iya bashi amsa, ba kuma wanda ya kara yi masa tambayoyi tun daga wannan rana.
46 E ninguém podia responder-lhe palavra; nem desde aquele dia jamais ousou alguém interrogá-lo.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.