Mateus 22

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NTLH

Sair da comparação
NTLH Nova Tradução na Linguagem de Hoje 2000
1 Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa,
1 De novo Jesus usou parábolas para falar ao povo. Ele disse:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa.
2 — O
3 Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.
3 Depois mandou os empregados chamarem os convidados, mas eles não quiseram vir.
4 “Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’
4 Então mandou outros empregados com o seguinte recado: “Digam aos convidados que tudo está preparado para a festa. Já matei os bezerros e os bois gordos, e tudo está pronto. Que venham à festa!”
5 “Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa.
5 — Mas os convidados não se importaram com o convite e foram tratar dos seus negócios: um foi para a sua fazenda, e outro, para o seu armazém.
6 Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su.
6 Outros agarraram os empregados, bateram neles e os mataram.
7 Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.
7 O rei ficou com tanta raiva, que mandou matar aqueles assassinos e queimar a cidade deles.
8 “Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba.
8 Depois chamou os seus empregados e disse: “A minha festa de casamento está pronta, mas os convidados não a mereciam.
9 Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’
9 Agora vão pelas ruas e convidem todas as pessoas que vocês encontrarem.”
10 Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.
10 — Então os empregados saíram pelas ruas e reuniram todos os que puderam encontrar, tanto bons como maus. E o salão de festas ficou cheio de gente.
11 “Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren.
11 Quando o rei entrou para ver os convidados, notou um homem que não estava usando roupas de festa
12 Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.
12 e perguntou: “Amigo, como é que você entrou aqui sem roupas de festa?”
13 “Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
13 Então o rei disse aos empregados: “Amarrem os pés e as mãos deste homem e o joguem fora, na escuridão. Ali ele vai chorar e ranger os dentes de desespero.”
14 “Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
14 E Jesus terminou, dizendo:
15 Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa.
15 Os fariseus saíram e fizeram um plano para conseguir alguma prova contra Jesus.
16 Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba.
16 Então mandaram que alguns dos seus seguidores e alguns membros do partido de Herodes fossem dizer a Jesus: — Mestre, sabemos que o senhor é honesto, ensina a verdade sobre a maneira de viver que Deus exige e não se importa com a opinião dos outros, nem julga pela aparência.
17 To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
17 Então o que o senhor acha: é ou não é contra a nossa Lei pagar impostos ao Imperador romano?
18 Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko?
18 Mas Jesus percebeu a malícia deles e respondeu:
19 Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari,
19 Tragam a moeda com que se paga o imposto! Trouxeram a moeda,
20 sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”
20 e ele perguntou:
21 Suka amsa, “Na Kaisar ne.”
21 Eles responderam: — São do Imperador. Então Jesus disse:
22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
22 Eles ficaram admirados quando ouviram isso. Então deixaram Jesus e foram embora.
23 A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
23 Naquele mesmo dia chegaram perto de Jesus alguns saduceus , afirmando que ninguém ressuscita.
24 Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya.
24 Eles disseram a Jesus: — Mestre, Moisés ensinou assim: “Se um homem morrer e deixar a esposa sem filhos, o irmão dele deve casar com a viúva, para terem filhos, que serão considerados filhos do irmão que morreu.”
25 A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
25 Acontece que havia entre nós sete irmãos. O mais velho casou e morreu sem deixar filhos. Assim, ele deixou a viúva para o segundo irmão.
26 Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
26 A mesma coisa aconteceu com este, e também com o terceiro, e, finalmente, com todos os sete.
27 A ƙarshe, macen ta mutu.
27 Depois de todos eles, a mulher também morreu.
28 To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
28 Portanto, no dia da ressurreição, de qual dos sete a mulher vai ser esposa? Pois todos eles casaram com ela!
29 Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba.
29 Jesus respondeu:
30 Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama.
30 Pois, quando os mortos ressuscitarem, serão como os anjos do céu, e ninguém casará.
31 Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne,
31 E, quanto à ressurreição dos mortos, será que vocês nunca leram o que Deus disse? Ele afirmou:
32 ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
32 “Eu sou o Deus de Abraão, o Deus de Isaque e o Deus de Jacó.” E Deus não é Deus dos mortos e sim dos vivos.
33 Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 Quando a multidão ouviu isso, ficou admirada com o ensinamento dele.
34 Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru.
34 Os fariseus se reuniram quando souberam que Jesus tinha feito os saduceus calarem a boca.
35 Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya.
35 E um deles, que era mestre da Lei , querendo conseguir alguma prova contra Jesus, perguntou:
36 “Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
36 — Mestre, qual é o mais importante de todos os mandamentos da Lei ?
37 Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’
37 Jesus respondeu:
38 Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma.
38 Este é o maior mandamento e o mais importante.
39 Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’
39 E o segundo mais importante é parecido com o primeiro: “Ame os outros como você ama a você mesmo.”
40 Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
40 Toda a Lei de Moisés e os ensinamentos dos
41 Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
41 Quando os fariseus estavam reunidos, Jesus perguntou a eles:
42 “Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?”
42 — O que vocês pensam sobre o — De Davi! — responderam eles.
43 Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
43 Jesus tornou a perguntar:
44 “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
44 “O Senhor Deus disse ao meu Senhor:
45 To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
45 Portanto, se Davi chama o Messias de Senhor, como é que o Messias pode ser descendente de Davi?
46 Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
46 Ninguém podia responder mais nada, e daquele dia em diante não tiveram coragem de lhe fazer mais perguntas.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.