Mateus 22
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NAA
1 Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa,
1 De novo Jesus lhes falou por parábolas, dizendo:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa.
2 — O Reino dos Céus é semelhante a um rei que preparou uma festa de casamento para seu filho.
3 Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.
3 Enviou os seus servos a chamar os convidados para a festa, mas estes não quiseram vir.
4 “Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’
4 Enviou ainda outros servos, dizendo: “Digam aos convidados: Eis que já preparei o meu banquete; os meus bois e animais da engorda já foram abatidos, e tudo está pronto; venham para a festa.”
5 “Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa.
5 Mas os convidados não se importaram e se foram, um para o seu campo, outro para o seu negócio.
6 Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su.
6 Outros, agarrando os servos, os maltrataram e mataram.
7 Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.
7 — O rei ficou furioso e, enviando as suas tropas, exterminou aqueles assassinos e incendiou a cidade deles.
8 “Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba.
8 Então disse aos seus servos: “A festa está pronta, mas os convidados não eram dignos.
9 Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’
9 Vão, pois, para as encruzilhadas dos caminhos e convidem para o banquete todos os que vocês encontrarem.”
10 Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.
10 E, saindo aqueles servos pelas estradas, reuniram todos os que encontraram, maus e bons; e a sala do banquete ficou cheia de convidados.
11 “Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren.
11 — Mas, quando o rei entrou para ver os que estavam à mesa, notou ali um homem que não trazia veste nupcial
12 Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.
12 e perguntou-lhe: “Amigo, como você entrou aqui sem veste nupcial?” E ele emudeceu.
13 “Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
13 Então o rei ordenou aos serventes: “Amarrem os pés e as mãos dele e atirem-no para fora, nas trevas; ali haverá choro e ranger de dentes.”
14 “Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
14 Porque muitos são chamados, mas poucos são escolhidos.
15 Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa.
15 Então os fariseus se retiraram e consultaram entre si como surpreenderiam Jesus em alguma palavra.
16 Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba.
16 E enviaram-lhe discípulos, juntamente com os herodianos, para lhe dizer: — Mestre, sabemos que o senhor é verdadeiro e que ensina o caminho de Deus de acordo com a verdade, sem se importar com a opinião dos outros, porque não olha para a aparência das pessoas.
17 To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
17 Assim sendo, diga-nos o que o senhor acha: é lícito pagar imposto a César ou não?
18 Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko?
18 Mas Jesus, percebendo a maldade deles, respondeu:
19 Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari,
19 Mostrem-me a moeda do imposto. Trouxeram-lhe um denário.
20 sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”
20 E Jesus lhes perguntou:
21 Suka amsa, “Na Kaisar ne.”
21 Eles responderam: — De César. Então Jesus lhes disse:
22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
22 Ouvindo isto, se admiraram e, deixando-o, foram embora.
23 A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
23 Naquele dia, alguns saduceus, que dizem não haver ressurreição, aproximaram-se de Jesus e lhe perguntaram:
24 Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya.
24 — Mestre, Moisés disse: “Se alguém morrer, não tendo filhos, o irmão desse homem deve casar com a viúva e gerar descendentes para o falecido.”
25 A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
25 Ora, havia entre nós sete irmãos. O primeiro, tendo casado, morreu e, não tendo descendência, deixou sua mulher para seu irmão.
26 Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
26 O mesmo aconteceu com o segundo, com o terceiro, até o sétimo.
27 A ƙarshe, macen ta mutu.
27 Por fim, depois de todos, morreu também a mulher.
28 To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
28 Portanto, na ressurreição, de qual dos sete ela será esposa? Porque todos casaram com ela.
29 Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba.
29 Jesus respondeu:
30 Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama.
30 Porque, na ressurreição, nem casam, nem se dão em casamento, mas são como os anjos no céu.
31 Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne,
31 Quanto à ressurreição dos mortos, vocês nunca leram o que Deus disse a vocês:
32 ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
32 “Eu sou o Deus de Abraão, o Deus de Isaque e o Deus de Jacó”? Ele não é Deus de mortos, e sim de vivos.
33 Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 Ouvindo isto, as multidões se maravilhavam da sua doutrina.
34 Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru.
34 Entretanto, os fariseus, sabendo que Jesus havia silenciado os saduceus, reuniram-se em conselho.
35 Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya.
35 E um deles, intérprete da Lei, querendo pôr Jesus à prova, perguntou-lhe:
36 “Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
36 — Mestre, qual é o grande mandamento na Lei?
37 Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’
37 Jesus respondeu:
38 Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma.
38 Este é o grande e primeiro mandamento.
39 Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’
39 E o segundo, semelhante a este, é: “Ame o seu próximo como você ama a si mesmo.”
40 Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
40 Destes dois mandamentos dependem toda a Lei e os Profetas.
41 Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
41 Estando reunidos os fariseus, Jesus lhes perguntou:
42 “Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?”
42 — O que vocês pensam do Cristo? De quem é filho? Eles responderam: — De Davi.
43 Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
43 E Jesus perguntou:
44 “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
44 “Disse o Senhor ao meu Senhor:
45 To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
45 — Portanto, se Davi o chama de Senhor, como ele pode ser filho de Davi?
46 Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
46 E ninguém podia lhe responder uma palavra; e a partir daquele dia ninguém mais ousou fazer perguntas.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.