Mateus 22

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs ARC

Sair da comparação
ARC Almeida Revista e Corrigida 2009
1 Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa,
1 Então, Jesus, tomando a palavra, tornou a falar-lhes em parábolas, dizendo:
2 “Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa.
2 O Reino dos céus é semelhante a um certo rei que celebrou as bodas de seu filho.
3 Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.
3 E enviou os seus servos a chamar os convidados para as bodas; e estes não quiseram vir.
4 “Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’
4 Depois, enviou outros servos, dizendo: Dizei aos convidados: Eis que tenho o meu jantar preparado, os meus bois e cevados
5 “Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa.
5 Porém eles, não fazendo caso, foram, um para o seu campo, e outro para o seu negócio;
6 Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su.
6 e, os outros, apoderando-se dos servos, os ultrajaram e mataram.
7 Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.
7 E o rei, tendo notícias e, enviando os seus exércitos, destruiu aqueles homicidas, e incendiou a sua cidade.
8 “Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba.
8 Então, disse aos servos: As bodas, na verdade, estão preparadas, mas os convidados não eram dignos.
9 Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’
9 Ide, pois, às saídas dos caminhos e convidai para as bodas a todos os que encontrardes.
10 Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.
10 E os servos, saindo pelos caminhos, ajuntaram todos quantos encontraram, tanto maus como bons; e a festa nupcial ficou cheia de convidados.
11 “Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren.
11 E o rei, entrando para ver os convidados, viu ali um homem
12 Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.
12 E disse-lhe: Amigo, como entraste aqui, não tendo veste nupcial? E ele emudeceu.
13 “Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’
13 Disse, então, o rei aos servos: Amarrai-o de pés e mãos, levai-o e lançai-
14 “Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”
14 Porque muitos são chamados, mas poucos, escolhidos.
15 Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa.
15 Então, retirando-se os fariseus, consultaram entre si como o surpreenderiam em alguma palavra.
16 Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba.
16 E enviaram-lhe os seus discípulos, com os herodianos, dizendo: Mestre, bem sabemos que és verdadeiro e ensinas o caminho de Deus, segundo a verdade, sem te importares com quem quer que seja, porque não olhas à aparência dos homens.
17 To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”
17 Dize-nos, pois, que te parece: é lícito pagar o tributo a César ou não?
18 Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko?
18 Jesus, porém, conhecendo a sua malícia, disse: Por que me experimentais, hipócritas?
19 Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari,
19 Mostrai-me a moeda do tributo. E eles lhe apresentaram um dinheiro.
20 sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”
20 E ele disse-lhes: De quem é esta efígie e
21 Suka amsa, “Na Kaisar ne.”
21 Disseram-lhe eles: De César. Então, ele lhes disse: Dai, pois, a César o que
22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.
22 E eles, ouvindo isso, maravilharam-se e, deixando-o, se retiraram.
23 A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya.
23 No mesmo dia, chegaram junto dele os saduceus, que dizem não haver ressurreição, e o interrogaram,
24 Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya.
24 dizendo: Mestre, Moisés disse: Se morrer alguém, não tendo filhos, casará o seu irmão com a mulher dele e suscitará descendência a seu irmão.
25 A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa.
25 Ora, houve entre nós sete irmãos; o primeiro, tendo casado, morreu e, não tendo descendência, deixou sua mulher a seu irmão.
26 Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai.
26 Da mesma sorte, o segundo, e o terceiro, até ao sétimo;
27 A ƙarshe, macen ta mutu.
27 por fim, depois de todos, morreu também a mulher.
28 To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”
28 Portanto, na ressurreição, de qual dos sete será a mulher, visto que todos a possuíram?
29 Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba.
29 Jesus, porém, respondendo, disse-lhes: Errais, não conhecendo as Escrituras, nem o poder de Deus.
30 Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama.
30 Porque, na ressurreição, nem casam, nem são dados em casamento; mas serão como os anjos no céu.
31 Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne,
31 E, acerca da ressurreição dos mortos, não tendes lido o que Deus vos declarou, dizendo:
32 ‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”
32 Eu sou o Deus de Abraão, o Deus de Isaque e o Deus de Jacó? Ora, Deus não é Deus dos mortos, mas dos vivos.
33 Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.
33 E, as turbas, ouvindo isso, ficaram maravilhadas da sua doutrina.
34 Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru.
34 E os fariseus, ouvindo que ele fizera emudecer os saduceus, reuniram-se no mesmo lugar.
35 Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya.
35 E um deles, doutor da lei, interrogou-o para o experimentar, dizendo:
36 “Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”
36 Mestre, qual é o grande mandamento da lei?
37 Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’
37 E Jesus disse-lhe: Amarás o Senhor, teu Deus, de todo o teu coração, e de toda a tua alma, e de todo o teu pensamento.
38 Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma.
38 Este é o primeiro e grande mandamento.
39 Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’
39 E o segundo, semelhante a este, Amarás o teu próximo como a ti mesmo.
40 Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”
40 Desses dois mandamentos dependem toda a lei e os profetas.
41 Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su,
41 E, estando reunidos os fariseus, interrogou-os Jesus,
42 “Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?”
42 dizendo: Que pensais vós do Cristo? De quem é filho? Eles disseram-lhe: De Davi.
43 Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,
43 Disse-lhes ele: Como é, então, que Davi, em espírito, lhe chama Senhor, dizendo:
44 “ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,
44 Disse o Senhor ao meu Senhor: Assenta-te à minha direita, até que eu ponha os teus inimigos por escabelo de teus pés.
45 To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?”
45 Se Davi, pois, lhe chama Senhor, como é seu filho?
46 Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.
46 E ninguém podia responder-lhe uma palavra, nem, desde aquele dia, ousou mais alguém interrogá-lo.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.