1 Crônicas 11

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs VC

Sair da comparação
VC Versão Católica
1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
1 Todo o Israel se reuniu com Davi em Hebron, e disse: Vê: nós somos teus ossos e tua carne.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’ ”
2 Já antes, quando Saul era rei, eras tu que conduzias os destinos de Israel. O Senhor, teu Deus, te disse: És tu que apascentarás Israel, meu povo, e serás tu o chefe de Israel, meu povo.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
3 Assim todos os anciãos de Israel vieram para junto do rei em Hebron, e Davi concluiu um pacto com eles em Hebron, diante do Senhor; e eles ungiram-no rei de Israel, segundo a palavra do Senhor, pronunciada por Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
4 Foi Davi com todo o Israel contra Jerusalém, isto é, Jebus, onde estavam os jebuseus, habitantes da terra.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
5 Os jebuseus disseram a Davi: Aqui tu não entrarás. Mas Davi se apoderou da fortaleza de Sião, isto é, da cidade de Davi.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
6 O primeiro, disse ele, seja quem for, que vencer os jebuseus, tornar-se-á chefe e príncipe. O primeiro que subiu foi Joab, filho de Sarvia, e tornou-se chefe.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
7 Davi instalou-se na fortaleza; é por isso que a chamaram cidade de Davi.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
8 Ele fortificou a cidade ao redor, desde Milo até seus arredores, e Joab restaurou o resto da cidade.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
9 Davi tornou-se cada vez maior, e o Deus dos exércitos estava com ele.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
10 Eis os chefes dos heróis que estavam a serviço de Davi e que o ajudaram com todo o Israel a assegurar seu domínio, a fim de fazê-lo rei, segundo a palavra do Senhor, com respeito a Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda.
11 Eis o número dos heróis que estavam a serviço de Davi: Jesbaão, chefe dos trinta: ele brandiu sua lança contra trezentos homens e os abateu de uma só vez.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
12 Depois deste, Eleazar, filho de Dodo, o aoíta, um dos três heróis.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
13 Estava ele com Davi em Fesdomim, onde os filisteus se tinham reunido para o combate. Lá havia uma terra plantada de cevada, e o exército fugia diante dos filisteus.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
14 Eles se postaram no meio do campo, defenderam-no e destroçaram os filisteus; e o Senhor assegurou uma grande vitória.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
15 Três dos trinta capitães desceram à rocha, para perto de Davi, junto da caverna de Odolão, enquanto o acampamento dos filisteus estava levantado no vale dos refains.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
16 Ora, Davi estava na caverna e havia uma guarnição de filisteus em Belém.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
17 Davi exprimiu um desejo: Quem me dará de beber, disse ele, da água da cisterna que está às portas de Belém?
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
18 Os três homens atravessaram acampamento dos filisteus e tiraram água da cisterna que está à porta de Belém. Eles tomaram e a levaram a Davi, mas Davi não quis bebê-la e fez dela uma libação ao Senhor:
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba.
19 Deus me livre, disse ele, de beber semelhante coisa! Haveria eu de beber o sangue desses homens? Pois foi arriscando a própria vida que ma trouxeram. E recusou bebê-la. Eis o que fizeram esses três bravos.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
20 Abisai, irmão de Joab, era o chefe dos três; brandiu sua lança contra trezentos homens; matou-os e adquiriu um nome entre os três.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
21 Era o mais considerado da segunda tríade e foi o seu chefe, mas não se igualou aos três primeiros;
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
22 Banaias, filho de Jojada, homem de valor e rico em altos feitos, originário de Cabseel, foi o que venceu os dois filhos de Ariel, de Moab. Foi ele também quem desceu e matou o leão na cisterna, num dia em que nevava.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
23 Foi ele ainda quem venceu um egípcio de cinco côvados de altura; esse egípcio tinha na mão uma lança semelhante a um cilindro de tear de tecelão. Foi contra ele com um bordão, arrancou-lhe a lança das mãos e o matou com a própria lança.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
24 Eis o que fez Banaias, filho de Jojada, que foi célebre entre os três valentes.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
25 Era mais considerado que os trinta; todavia não se igualou aos três. Davi o colocou à testa de sua guarda.
26 Jarumawan nan su ne,
26 Valentes homens do exército: Asael, irmão de Joab; Elcanã, filho de Dodo, de Belém;
27 Shammot mutumin Haror,
27 Samot, de Aori; Heles, de Falon:
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa,
28 Hira, filho de Aces, de Técua;
29 Sibbekai mutumin Husha,
29 Abieser, de Anatot; Sobocai, o husatita; Ilai, o aoíta; Maarai, de Netofa;
30 Maharai mutumin Netofa,
30 Heled, filho de Baana, de Netofa;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin,
31 Etai, filho de Ribai, de Gabaa, dos filhos de Benjamim; Banaia, de Faraton;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash,
32 Hurai, dos vales de Gaas; Abiel, de Araba; Azmavet, de Baurão; Eliaba, de Salabon; Bené-Assem de Gezon;
33 Azmawet mutumin Harum,
33 Jonatã, filho de Sage, de Arar;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza,
34 Aião, filho de Sacar, de Arar;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar,
35 Elifal, filho de Ur; Hefer, de Mequera;
36 Hefer mutumin Mekerat,
36 Aia, de Felon; Hesro, de Carmelo;
37 Hezro mutumin Karmel,
37 Naarai, filho de Asbai; Joel, irmão de Natã;
38 Yowel ɗan’uwan Natan,
38 Mibaar, filho de Agarai;
39 Zelek mutumin Ammon
39 Selec, o amonita; Naarai, de Berot, escudeiro de Joab, filho de Sarvia;
40 Ira mutumin Itra,
40 Ira, de Jeter; Gareb, de Jeter;
41 Uriya mutumin Hitti
41 Urias, o hiteu; Zabad, filho de Ooli;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
42 Adina, filho de Siza, filho de Rubem, chefe dos rubenitas, e com ele trinta homens;
43 Hanan ɗan Ma’aka,
43 Hanã, filho de Maaca; Josafá, de Matã;
44 Uzziya mutumin Ashtarot,
44 Ozías, de Astarot; Sarna e Jeiel, filhos de Hotão, de Aroer;
45 Yediyayel ɗan Shimri,
45 Jediel, filho de Samri; Joa, seu irmão, o tosaíta;
46 Eliyel mutumin Ma’aha,
46 Eliel, de Maum; Jeribai e Josaia, filhos de Elnaem; Jetma, o moabita;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
47 Eliel, Obed e Jasiel, de Masobia.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 11, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.