1 Crônicas 11
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVI
1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
1 Todo o Israel reuniu-se com Davi em Hebrom e disse: "Somos sangue do teu sangue.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’ ”
2 No passado, mesmo quando Saul era rei, eras tu quem liderava Israel em suas batalhas. E o Senhor, o teu Deus, te disse: ‘Você pastoreará o meu povo Israel, e será o seu governante’ ".
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
3 Então todas as autoridades de Israel foram ao encontro do rei Davi em Hebrom, e ele fez um acordo com eles em Hebrom perante o Senhor, e eles ungiram Davi rei de Israel, conforme o Senhor havia anunciado por meio de Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
4 Davi e todos os israelitas marcharam para Jerusalém, que é Jebus. Os jebuseus, habitantes da cidade,
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
5 disseram a Davi: "Você não entrará aqui". No entanto, Davi conquistou a fortaleza de Sião, a cidade de Davi.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
6 Naquele dia Davi tinha dito: "O primeiro que atacar os jebuseus se tornará o comandante do exército". Joabe, filho de Zeruia, foi o primeiro, e por isso recebeu o comando do exército.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
7 Davi passou a morar na fortaleza, e por isso ela foi chamada cidade de Davi.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
8 Ele reconstruiu a cidade ao redor da fortaleza, desde os muros de arrimo até os muros ao redor, e Joabe restaurou o restante da cidade.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
9 E Davi foi se tornando cada vez mais poderoso, pois o Senhor dos Exércitos estava com ele.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
10 Estes foram os chefes dos principais guerreiros de Davi, que junto com todo Israel, deram um grande apoio para estender o seu reinado a todo o país, conforme o Senhor havia prometido.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda.
11 Esta é a lista deles: Jasobeão, um hacmonita, era o chefe dos oficiais; foi ele que, empunhando sua lança, matou trezentos homens numa mesma batalha.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
12 Depois, Eleazar, filho de Dodô, de Aoí, um dos três principais guerreiros.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
13 Ele estava com Davi na plantação de cevada de Pas-Damim, onde os filisteus se reuniram para a guerra. As tropas israelitas fugiram dos filisteus,
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
14 mas eles mantiveram sua posição no meio da plantação. Eles o defenderam e feriram os filisteus, e o Senhor lhes deu uma grande vitória.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
15 Quando um grupo de filisteus estava acampado no vale de Refaim, três chefes do pelotão dos trinta foram encontrar Davi na rocha que há perto da caverna de Adulão.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
16 Estando Davi nessa fortaleza, e o destacamento filisteu em Belém,
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
17 Davi expressou seu desejo: "Quem me dera me trouxessem água da cisterna que fica junto à porta de Belém! "
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
18 Então aqueles três infiltraram-se no acampamento filisteu, tiraram água daquela cisterna e a trouxeram a Davi. Mas ele se recusou a beber; em vez disso, derramou-a como uma oferta ao Senhor.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba.
19 "Longe de mim fazer isso, ó meu Deus! ", disse Davi. "Esta água representa o sangue desses homens que arriscaram a própria vida! " Eles arriscaram a vida para trazê-la. E não quis bebê-la. Foram essas as proezas dos três principais guerreiros.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
20 Abisai, o irmão de Joabe, era o chefe do batalhão dos trinta. Com uma lança enfrentou trezentos homens e os matou, tornando-se tão famoso quanto os três.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
21 Foi honrado duas vezes mais do que o batalhão dos trinta, e se tornou chefe deles, mas nunca igualou-se aos três principais guerreiros.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
22 Benaia, filho de Joiada, era um corajoso soldado de Cabzeel, e realizou grandes feitos. Matou dois dos melhores guerreiros de Moabe e, num dia de neve, desceu em uma cova e matou um leão.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
23 Também matou um egípcio de dois metros e vinte e cinco centímetros de altura. Embora o egípcio tivesse na mão uma lança parecida com uma lançadeira de tecelão, Benaia o enfrentou com um cajado. Arrancou a lança da mão do egípcio e com ela o matou.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
24 Esses foram os grandes feitos de Benaia, filho de Joiada, que também foi tão famoso quanto os três principais guerreiros de Davi.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
25 Foi mais honrado do que qualquer dos trinta, mas nunca igualou-se aos três. E Davi lhe deu o comando da sua guarda pessoal.
26 Jarumawan nan su ne,
26 Os outros guerreiros foram: Asael, irmão de Joabe; Elanã, filho de Dodô, de Belém;
27 Shammot mutumin Haror,
27 Samote, de Haror; Helez, de Pelom;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa,
28 Ira, filho de Iques, de Tecoa; Abiezer, de Anatote;
29 Sibbekai mutumin Husha,
29 Sibecai, de Husate; Ilai, de Aoí;
30 Maharai mutumin Netofa,
30 Maarai, de Netofate; Helede, filho de Baaná, de Netofate;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin,
31 Itai, filho de Ribai, de Gibeá de Benjamim; Benaia, de Piratom;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash,
32 Hurai, dos riachos de Gaás; Abiel, de Arbate;
33 Azmawet mutumin Harum,
33 Azmavete, de Baarum; Eliaba, de Saalbom;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza,
34 os filhos de Hasém, de Gizom; Jônatas, filho de Sage, de Harar;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar,
35 Aião, filho de Sacar, de Harar; Elifal, filho de Ur;
36 Hefer mutumin Mekerat,
36 Héfer, de Mequerate; Aías, de Pelom;
37 Hezro mutumin Karmel,
37 Hezro, de Carmelo; Naarai, filho de Ezbai;
38 Yowel ɗan’uwan Natan,
38 Joel, irmão de Natã; Mibar, filho de Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon
39 o amonita Zeleque; Naarai, de Beerote, escudeiro de Joabe, filho de Zeruia;
40 Ira mutumin Itra,
40 Ira e Garebe, de Jatir;
41 Uriya mutumin Hitti
41 Urias, o hitita; Zabade, filho de Alai;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
42 Adina, filho de Siza, de Rúben, chefe dos rubenitas e do grupo dos trinta;
43 Hanan ɗan Ma’aka,
43 Hanã, filho de Maaca; Josafá, de Mitene;
44 Uzziya mutumin Ashtarot,
44 Uzia, de Asterate; Sama e Jeiel, filhos de Hotão, de Aroer;
45 Yediyayel ɗan Shimri,
45 Jediael, filho de Sinri; seu irmão, Joá, de Tiz;
46 Eliyel mutumin Ma’aha,
46 Eliel, de Maave; Jeribai e Josavias, filhos de Elnaão; Itma, um moabita,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
47 e Eliel, Obede e Jaasiel, de Mezoba.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 11, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.