Lucas 1

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVI

Sair da comparação
NVI Nova Versão Internacional
1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
1 Muitos já se dedicaram a elaborar um relato dos fatos que se cumpriram entre nós,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
2 conforme nos foram transmitidos por aqueles que desde o início foram testemunhas oculares e servos da palavra.
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
3 Eu mesmo investiguei tudo cuidadosamente, desde o começo, e decidi escrever-te um relato ordenado, ó excelentíssimo Teófilo,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
4 para que tenhas a certeza das coisas que te foram ensinadas.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma ’yar zuriyar Haruna ce.
5 No tempo de Herodes, rei da Judéia, havia um sacerdote chamado Zacarias, que pertencia ao grupo sacerdotal de Abias; Isabel, sua mulher, também era descendente de Arão.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
6 Ambos eram justos aos olhos de Deus, obedecendo de modo irrepreensível a todos os mandamentos e preceitos do Senhor.
7 Sai dai ba su da ’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
7 Mas eles não tinham filhos, porque Isabel era estéril; e ambos eram de idade avançada.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
8 Certa vez, estando de serviço o seu grupo, Zacarias estava servindo como sacerdote diante de Deus.
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
9 Ele foi escolhido por sorteio, de acordo com o costume do sacerdócio, para entrar no santuário do Senhor e oferecer incenso.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
10 Chegando a hora de oferecer incenso, o povo todo estava orando do lado de fora.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
11 Então um anjo do Senhor apareceu a Zacarias, à direita do altar do incenso.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
12 Quando Zacarias o viu, perturbou-se e foi dominado pelo medo.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
13 Mas o anjo lhe disse: "Não tenha medo, Zacarias; sua oração foi ouvida. Isabel, sua mulher, lhe dará um filho, e você lhe dará o nome de João.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
14 Ele será motivo de prazer e de alegria para você, e muitos se alegrarão por causa do nascimento dele,
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
15 pois será grande aos olhos do Senhor. Ele nunca tomará vinho nem bebida fermentada, e será cheio do Espírito Santo desde antes do seu nascimento.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
16 Fará retornar muitos dentre o povo de Israel ao Senhor, o seu Deus.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga ’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
17 E irá adiante do Senhor, no espírito e no poder de Elias, para fazer voltar o coração dos pais a seus filhos e os desobedientes à sabedoria dos justos, para deixar um povo preparado para o Senhor".
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
18 Zacarias perguntou ao anjo: "Como posso ter certeza disso? Sou velho, e minha mulher é de idade avançada".
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
19 O anjo respondeu: "Sou Gabriel, o que está sempre na presença de Deus. Fui enviado para lhe transmitir estas boas novas.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
20 Agora você ficará mudo. Não poderá falar até o dia em que isso acontecer, porque não acreditou em minhas palavras, que se cumprirão no tempo oportuno".
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
21 Enquanto isso, o povo esperava por Zacarias, estranhando sua demora no santuário.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
22 Quando saiu, não conseguia falar nada; o povo percebeu então que ele tivera uma visão no santuário. Zacarias fazia sinais para eles, mas permanecia mudo.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
23 Quando se completou seu período de serviço, ele voltou para casa.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
24 Depois disso, Isabel, sua mulher, engravidou e durante cinco meses não saiu de casa.
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
25 E ela dizia: "Isto é obra do Senhor fez! Agora ele olhou para mim com favor, para desfazer a minha humilhação perante o povo. "
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
26 No sexto mês Deus enviou o anjo Gabriel a Nazaré, cidade da Galiléia,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
27 a uma virgem prometida em casamento a certo homem chamado José, descendente de Davi. O nome da virgem era Maria.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
28 O anjo, aproximando-se dela, disse: "Alegre-se, agraciada! O Senhor está com você! "
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
29 Maria ficou perturbada com essas palavras, pensando no que poderia significar esta saudação.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
30 Mas o anjo lhe disse: "Não tenha medo, Maria; você foi agraciada por Deus!
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
31 Você ficará grávida e dará à luz um filho, e lhe porá o nome de Jesus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
32 Ele será grande e será chamado Filho do Altíssimo. O Senhor Deus lhe dará o trono de seu pai Davi,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.”
33 e ele reinará para sempre sobre o povo de Jacó; seu Reino jamais terá fim".
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
34 Perguntou Maria ao anjo: "Como acontecerá isso, se sou virgem? "
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
35 O anjo respondeu: "O Espírito Santo virá sobre você, e o poder do Altíssimo a cobrirá com a sua sombra. Assim, aquele que há de nascer será chamado santo, Filho de Deus.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
36 Também Isabel, sua parenta, terá um filho na velhice; aquela que diziam ser estéril já está em seu sexto mês de gestação.
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
37 Pois nada é impossível para Deus".
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
38 Respondeu Maria: "Sou serva do Senhor; que aconteça comigo conforme a tua palavra". Então o anjo a deixou.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
39 Naqueles dias, Maria preparou-se e foi depressa para a uma cidade da região montanhosa da Judéia,
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
40 onde entrou na casa de Zacarias e saudou Isabel.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
41 Quando Isabel ouviu a saudação de Maria, o bebê agitou-se em seu ventre, e Isabel ficou cheia do Espírito Santo.
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
42 Em alta voz exclamou: "Bendita é você entre as mulheres, e bendito é o filho que você dará à luz!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
43 Mas por que sou tão agraciada, a ponto de me visitar a mãe do meu Senhor?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
44 Logo que a sua saudação chegou aos meus ouvidos, o bebê que está em meu ventre agitou-se de alegria.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
45 Feliz é aquela que creu que se cumprirá aquilo que o Senhor lhe disse! "
46 Sai Maryamu ta ce,
46 Então disse Maria: "Minha alma engrandece ao Senhor
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
47 e o meu espírito se alegra em Deus, meu Salvador,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa.
48 pois atentou para a humildade da sua serva. De agora em diante, todas as gerações me chamarão bem-aventurada,
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa,
49 pois o Poderoso fez grandes coisas em meu favor; santo é o seu nome.
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa,
50 A sua misericórdia estende-se aos que o temem, de geração em geração.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa;
51 Ele realizou poderosos feitos com seu braço; dispersou os que são soberbos no mais íntimo do coração.
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu
52 Derrubou governantes dos seus tronos, mas exaltou os humildes.
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa
53 Encheu de coisas boas os famintos, mas despediu de mãos vazias os ricos.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila,
54 Ajudou a seu servo Israel, lembrando-se da sua misericórdia
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada,
55 para com Abraão e seus descendentes para sempre, como dissera aos nossos antepassados".
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
56 Maria ficou com Isabel cerca de três meses e depois voltou para casa.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
57 Ao se completar o tempo de Isabel dar à luz, ela teve um filho.
58 Maƙwabtanta da ’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
58 Seus vizinhos e parentes ouviram falar da grande misericórdia que o Senhor lhe havia demonstrado e se alegraram com ela.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
59 No oitavo dia foram circuncidar o menino e queriam dar-lhe o nome do pai, Zacarias;
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
60 mas sua mãe tomou a palavra e disse: "Não! Ele será chamado João".
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
61 Disseram-lhe: "Você não há nenhum parente com esse nome".
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
62 Então fizeram sinais ao pai do menino, para saber como queria que a criança se chamasse.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
63 Ele pediu uma tabuinha e, para admiração de todos, escreveu: "O nome dele é João".
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
64 Imediatamente sua boca se abriu, sua língua se soltou e ele começou a falar, louvando a Deus.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
65 Todos os vizinhos ficaram cheios de temor, e por toda a região montanhosa da Judéia se falava sobre essas coisas.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
66 Todos os que ouviam falar disso se perguntavam: "O que vai ser este menino? " Pois a mão do Senhor estava com ele.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
67 Seu pai, Zacarias, foi cheio do Espírito Santo e profetizou:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila,
68 "Louvado seja o Senhor, o Deus de Israel, porque visitou e redimiu o seu povo.
69 Ya tā mana ƙahon ceto
69 Ele promoveu poderosa salvação para nós, na linhagem do seu servo Davi,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki),
70 ( como falara pelos seus santos profetas, na antigüidade ),
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu
71 salvando-nos dos nossos inimigos e da mão de todos os que nos odeiam,
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu,
72 para mostrar sua misericórdia aos nossos antepassados e lembrar sua santa aliança,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
73 o juramento que fez ao nosso pai Abraão:
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu,
74 resgatar-nos da mão dos nossos inimigos para servi-lo sem medo,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
75 em santidade e justiça, diante dele todos os nossos dias.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki;
76 E você, menino, será chamado profeta do Altíssimo, pois irá adiante do Senhor, para lhe preparar o caminho,
77 don ka sanar da mutanensa ceto,
77 para dar ao seu povo o conhecimento da salvação, mediante o perdão dos seus pecados,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna,
78 por causa das ternas misericórdias de nosso Deus, pelas quais do alto nos visitará o sol nascente
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu,
79 para brilhar sobre aqueles que estão vivendo nas trevas e na sombra da morte, e guiar nossos pés no caminho da paz".
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
80 E o menino crescia e se fortalecia no espírito; e viveu no deserto, até aparecer publicamente a Israel.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Lucas 1, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.