Levítico 22
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NAA
1 Ubangiji ya ce wa Musa,
1 O Senhor disse a Moisés:
2 “Faɗa wa Haruna da ’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
2 — Diga a Arão e aos seus filhos que se abstenham das ofertas sagradas, dedicadas a mim pelos filhos de Israel, para que não profanem o meu santo nome. Eu sou o Senhor .
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
3 Diga-lhes: Ao longo de suas gerações, qualquer descendente de vocês que se aproximar das ofertas sagradas que os filhos de Israel dedicam ao Senhor , tendo sobre si a sua impureza, será eliminado da minha presença. Eu sou o Senhor .
4 “ ‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
4 — Ninguém da descendência de Arão que for leproso ou tiver fluxo comerá das ofertas sagradas, até que esteja puro. Também não poderá comer das ofertas sagradas o que tocar alguma coisa impura por causa de um morto ou aquele que tiver emissão de sêmen;
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
5 nem aquele que tocar algum animal que rasteja pelo chão, com o que se faz impuro, ou alguma pessoa, com a qual se faz impuro, seja qual for a impureza dessa pessoa.
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
6 Quem tocar em tais coisas ficará impuro até a tarde e não comerá das ofertas sagradas sem primeiro banhar o seu corpo em água.
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
7 Depois do pôr do sol estará puro e poderá comer das ofertas sagradas, porque este é o seu alimento.
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
8 Do animal que morre por si mesmo ou é dilacerado por outro animal não comerá, para não se contaminar com isso. Eu sou o Senhor .
9 “ ‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
9 Guardarão, pois, a obrigação que têm para comigo, para que, por isso, não levem sobre si pecado e morram, havendo feito profanação. Eu sou o Senhor , que os santifico.
10 “ ‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
10 — Nenhum estranho poderá comer das ofertas sagradas; nem o hóspede do sacerdote nem o seu trabalhador diarista poderão comer das ofertas sagradas.
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
11 Mas, se o sacerdote comprar algum escravo com o seu dinheiro, este poderá comer delas; os que nascerem na casa do sacerdote, estes poderão comer do seu pão.
12 In ’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
12 Se a filha do sacerdote se casar com um estranho, ela não poderá comer da oferta das coisas sagradas.
13 Amma idan ’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da ’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
13 Mas, se a filha do sacerdote for viúva ou divorciada, não tiver filhos e tiver voltado à casa de seu pai, como na sua mocidade, poderá comer do pão de seu pai; mas nenhum estranho poderá comer desse alimento.
14 “ ‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
14 — Se alguém, por engano, comer a oferta sagrada, deverá acrescentar a ela a sua quinta parte e a dará ao sacerdote com a oferta sagrada.
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
15 Os sacerdotes não devem profanar as coisas sagradas que os filhos de Israel oferecem ao Senhor ,
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’ ”
16 pois assim os fariam levar sobre si a culpa da iniquidade, comendo as ofertas sagradas; porque eu sou o Senhor , que os santifico.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
17 O Senhor disse a Moisés:
18 “Yi wa Haruna da ’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
18 — Fale a Arão, a seus filhos e a todos os filhos de Israel e diga-lhes: Quando um homem da casa de Israel ou dos estrangeiros em Israel apresentar a sua oferta ao Senhor em holocausto, quer em cumprimento de seus votos ou como ofertas voluntárias,
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
19 para que seja aceitável deverá oferecer um macho sem defeito, seja do gado, do rebanho de ovelhas ou de cabras.
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
20 Porém todo o que tiver defeito, esse vocês não poderão oferecer; porque não seria aceito em favor de vocês.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
21 Quando alguém oferecer sacrifício pacífico ao Senhor , quer em cumprimento de voto ou como oferta voluntária, do gado ou do rebanho, o animal deve ser sem defeito para ser aceitável; nele, não poderá haver defeito nenhum.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
22 O cego, aleijado, mutilado, ulceroso, sarnoso ou cheio de feridas na pele, vocês não os devem oferecer ao Senhor e deles não devem apresentar como oferta queimada ao Senhor sobre o altar.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
23 Porém novilho ou cordeiro desproporcionados vocês poderão oferecer por oferta voluntária, mas não será aceito se for para cumprir um voto.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
24 Não ofereçam ao Senhor animal que tiver os testículos machucados, moídos, arrancados ou cortados; não façam isso em sua terra.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’ ”
25 Também da mão de um estrangeiro nenhum desses animais vocês poderão oferecer como pão do Deus de vocês, porque são corrompidos pelo defeito que há neles; não serão aceitos em favor de vocês.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
26 O Senhor disse ainda a Moisés:
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
27 — Quando nascer um bezerro, um cordeiro ou um cabrito, ele ficará sete dias com a mãe dele; do oitavo dia em diante será aceito por oferta queimada ao Senhor .
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
28 Quer seja vaca ou ovelha, não mate a ela e seu filhote, ambos no mesmo dia.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
29 Quando vocês oferecerem sacrifício de ação de graças ao Senhor , façam-no para que vocês sejam aceitos.
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
30 No mesmo dia, será comido; e, dele, não deixem ficar nada até a manhã seguinte. Eu sou o Senhor .
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
31 — Guardem e cumpram os meus mandamentos. Eu sou o Senhor .
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
32 Não profanem o meu santo nome, mas serei santificado no meio dos filhos de Israel. Eu sou o Senhor , que os santifico,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
33 que os tirei da terra do Egito, para ser o Deus de vocês. Eu sou o Senhor .
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Levítico 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.