Josué 6

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Ƙofofin Yeriko kuwa a kulle suke ciki da waje saboda Isra’ilawa, ba mai fita babu kuma mai shiga.
1 Então, Jericó estava firmemente fechada por causa dos filhos de Israel; ninguém saía e ninguém entrava.
2 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ba ka nasara a kan Yeriko, duk da sarkinta da mayaƙanta.
2 E o ­SENHOR disse a Josué: Vê, tenho dado na tua mão Jericó, e o seu rei, e os homens fortes e valentes.
3 Da kai da dukan sojoji, ku zaga birnin sau ɗaya kullum. Ku yi haka har kwana shida.
3 E vós rodeareis a cidade, todos vós homens de guerra, e andareis ao redor da cidade uma vez. Assim farás tu por seis dias.
4 Ka sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni raguna su kasance a gaban akwatin alkawari. A rana ta bakwai sai ku zaga birnin sau bakwai, firistocin suna busa ƙahoni.
4 E sete sacerdotes carregarão diante da arca sete trombetas de chifre de carneiro; e no sétimo dia rodeareis a cidade sete vezes, e os sacerdotes soprarão as trombetas.
5 Sa’ad da kuka ji sun ɗauki dogon lokaci suna busa ƙaho, sai mutane gaba ɗaya su tā da murya su yi ihu da ƙarfi; katangar birnin kuwa za tă rushe, sai sojoji su haura, ko wanne yă nufi inda ya fuskanta kai tsaye.”
5 E sucederá que, quando eles derem um longo toque com o chifre do carneiro, e quando ouvirdes o som da trombeta, todo o povo gritará com um alto brado; e o muro da cidade cairá completamente, e o povo subirá cada homem direto à sua frente.
6 Yoshuwa ɗan Nun kuwa ya kira firistoci ya ce musu, “Ku ɗauki akwatin alkawari, ku sa firistoci guda bakwai su riƙe ƙahoni su kasance a gabansa.”
6 E Josué, o filho de Num, chamou os sacerdotes, e disse-lhes: Tomai a arca do pacto, e que sete sacerdotes carreguem sete trombetas de chifres de carneiros diante da arca do ­SENHOR.
7 Sai ya umarci jama’a ya ce, “Mu je zuwa! Ku zaga birnin, masu tsaro da makamai su shiga gaban akwatin alkawarin Ubangiji.”
7 E ele disse ao povo: Passai adiante e rodeai a cidade, e aquele que estiver armado passe adiante da arca do ­SENHOR.
8 Da Yoshuwa ya gama yin wa mutane magana, sai firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai a gaban Ubangiji suka sha gaba suna busa ƙahoninsu, akwatin alkawari kuwa yana biye da su.
8 E sucedeu que, quando Josué havia falado ao povo, os sete sacerdotes que levavam as sete trombetas de chifres de carneiros passaram adiante do ­SENHOR, e sopraram as trombetas; e a arca do pacto do ­SENHOR os seguiu.
9 Masu tsaro da makamai kuma suna gaban firistoci waɗanda suke busa ƙahoni, masu tsaro daga baya kuma suna bin akwatin alkawari, ana ta busa ƙahoni.
9 E os homens armados foram diante dos sacerdotes que sopravam as trombetas, e a retaguarda vinha após a arca, com os sacerdotes indo avante e soprando as trombetas.
10 Amma Yoshuwa ya umarci mutane ya ce, “Kada ku yi kururuwar yaƙi, kada ku tā da murya, kada ku ce kome, sai ranar da na ce ku yi ihu, a sa’an nan ne sai ku yi ihu!”
10 E Josué havia ordenado ao povo, dizendo: Vós não gritareis, nem fareis qualquer ruído com a vossa voz, tampouco sairá da vossa boca qualquer palavra até o dia em que eu vos ordenar a gritar; então gritareis.
11 Sai ya sa aka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji aka kewaye birnin da shi sau ɗaya, sa’an nan mutane suka dawo masauƙinsu suka kwana a can.
11 Assim, a arca do ­SENHOR rodeou a cidade, indo em seu redor uma vez; e eles vieram ao acampamento, e se alojaram no acampamento.
12 Kashegari, Yoshuwa ya tashi da sassafe, firistoci kuma suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji.
12 E Josué se levantou de manhã cedo, e os sacerdotes tomaram a arca do ­SENHOR.
13 Firistoci guda bakwai waɗanda suke riƙe da ƙahoni guda bakwai suka shiga gaba, suna takawa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji suna kuma busa ƙahoni, masu tsaro ɗauke da makamai suna gabansu, sai masu tsaro da suke baya suna biye da akwatin alkawarin Ubangiji.
13 E sete sacerdotes, portando sete trombetas de chifres de carneiros diante da arca do ­SENHOR, seguiam continuamente e sopravam as trombetas; e os homens armados seguiam adiante deles; mas a retaguarda vinha após a arca do ­SENHOR, os sacerdotes iam à frente soprando as trombetas.
14 A rana ta biyu suka sāke zaga birnin sau ɗaya, suka kuma koma masauƙinsu. Haka suka yi har kwana shida.
14 E, no segundo dia, eles rodearam a cidade uma vez, e retornaram ao acampamento; assim o fizeram por seis dias.
15 A rana ta bakwai, suka tashi da sassafe suka zaga birnin sau bakwai yadda suka saba. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai.
15 E sucedeu que, no sétimo dia, eles se levantaram cedo, ao raiar do dia, e rodearam a cidade da mesma forma sete vezes; só naquele dia eles rodearam a cidade sete vezes.
16 A zagawa ta bakwai, da firistoci suka busa ƙahoni, sai Yoshuwa ya ba sojojin umarni ya ce, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin!
16 E sucedeu que, na sétima vez, quando os sacerdotes sopraram as trombetas, Josué disse ao povo: Gritai, pois o ­SENHOR vos entregou a cidade.
17 Birnin da dukan abin da yake cikinta za a miƙa su ga Ubangiji. Rahab karuwan nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye ’yan leƙen asirin ƙasa da muka aika.
17 E a cidade será amaldiçoada diante do ­SENHOR, ela e tudo o que nela está, só Raabe, a prostituta, viverá; ela e todos os que com ela estiverem na sua casa, porque ela escondeu os mensageiros que enviamos.
18 Amma, ba za ku ɗauki wani abin da za a hallaka ba, idan kuka yi haka, za ku jawo masifa da hallaka a kan mutanen Isra’ila a inda kuka sauka.
18 E vós, com toda sabedoria, guardai-vos das coisas amaldiçoadas, para que não vos torneis malditos a vós, ao tomarem alguma coisa maldita, e ao fazerem com que o acampamento de Israel se torne maldito, e o perturbeis.
19 Dukan azurfa da zinariya, da kwanonin tagulla da na ƙarfe, keɓaɓɓu ne ga Ubangiji, dole a sa su cikin ma’ajin Ubangiji.”
19 Mas toda a prata, e ouro e vasos de bronze e ferro, são consagrados ao ­SENHOR; eles virão para o tesouro do ­SENHOR.
20 Da aka busa ƙahoni, sojoji suka yi ihu, da jin ƙarar ƙahoni, mutane suka kuma yi ihu, sai katangar ta rushe; dukan mutanen kuwa suka shiga birnin kai tsaye, suka yi nasara a kanta.
20 Assim, o povo gritou quando os sacerdotes sopraram as trombetas; e sucedeu que, quando o povo ouviu o som da trombeta, o povo gritou com um grande brado, o muro caiu completamente, de forma que o povo subiu para a cidade, cada homem direto à sua frente, e tomaram a cidade.
21 Suka miƙa wa Ubangiji birnin, suka hallaka kowane abu mai ran da yake cikin birnin da takobi, maza da mata, yara da tsofaffi, shanu, tumaki da jakuna.
21 E tudo o que estava na cidade, eles destruíram por completo a fio de espada; tanto homem, como mulher, jovem e velho, boi, ovelha e jumento.
22 Yoshuwa ya ce wa mutanen nan biyu waɗanda suka je leƙen asirin ƙasar, “Ku shiga gidan karuwan nan ku fitar da ita da duk waɗanda suke nata bisa ga alkawarin da kuka yi mata.”
22 Entretanto, Josué havia dito aos dois homens que haviam espionado a região: Ide à casa da prostituta, e de lá tragam a mulher, e tudo o que ela possuir, como lhe jurastes.
23 Sai samarin waɗanda suka je leƙen asirin suka shiga suka fitar da Rahab, mahaifinta da mahaifiyarta, da ’yan’uwanta da duk abin da yake nata. Suka fitar da iyalinta gaba ɗaya suka sa su a wani wuri, ba a cikin masauƙin Isra’ilawa ba.
23 E os jovens espias entraram, e trouxeram Raabe, o seu pai, a sua mãe, os seus irmãos, e tudo o que ela possuía; e retiraram de lá toda a sua parentela, e os deixaram fora do acampamento de Israel.
24 Sa’an nan suka ƙona birnin tare da dukan abin da yake ciki tatas, amma suka sa azurfa da zinariya da kayan tagulla da na ƙarfe a cikin ma’aji na haikalin Ubangiji.
24 E a cidade, e tudo que nela estava, queimaram a fogo; somente a prata, o ouro e os vasos de bronze e de ferro, eles colocaram no tesouro da casa do ­SENHOR.
25 Amma Yoshuwa ya bar Rahab karuwan nan bai kashe ta ba, ita da iyalinta da duk abin da yake nata, domin ita ta ɓoye mutanen da Yoshuwa ya aika Yeriko don su leƙo asirin ƙasar kuma ta zauna tare da Isra’ilawa har wa yau.
25 E Josué salvou a vida de Raabe, a prostituta, e a casa do seu pai, e tudo o que ela possuía; e ela habitou em Israel até este dia; porque ela escondeu os mensageiros que Josué enviou para espionar Jericó.
26 A lokacin nan Yoshuwa ya yi wannan alkawari cewa, “Ubangiji zai tsine wa mutumin da zai yi ƙoƙarin sāke gina birnin nan, Yeriko.
26 E Josué os adjurou naquele tempo, dizendo: Maldito seja diante do ­SENHOR o homem que levantar e edificar esta cidade de Jericó; ele há de lançar o seu fundamento no seu primogênito, e no seu filho mais novo haverá de colocar as suas portas.
27 Ubangiji ya kasance tare da Yoshuwa, aka kuma san da shi a duk fāɗin ƙasar.
27 Assim, o ­SENHOR estava com Josué; e a sua fama foi alardeada por toda a nação.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Josué 6, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.