Ezequiel 46

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 “ ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
1 Assim diz o Senhor DEUS: O portão do átrio interno que olha em direção ao leste ficará fechado pelos seis dias de trabalho, mas no shabat ele será aberto, e no dia de lua nova ele será aberto.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
2 E o príncipe entrará pelo caminho do alpendre daquele portão, por fora, e ficará de pé junto ao pilar do portão, e os sacerdotes prepararão as suas ofertas queimadas, e as suas ofertas de paz, e ele adorará na soleira do portão, então ele irá adiante, mas o portão não será fechado até a noite.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
3 Da mesma forma, o povo da terra adorará à entrada deste portão, diante do SENHOR, nos shabats e nas luas novas.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci ’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
4 E a oferta queimada, que o príncipe oferecer ao SENHOR no dia do shabat, será de seis cordeiros sem defeito e um carneiro sem defeito.
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da ’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
5 E a oferta de alimento será de um efa por carneiro; e a oferta de alimento, pelos cordeiros, como ele for capaz de dar, de um him de azeite para cada efa.
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi, ’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
6 E no dia da lua nova será um novilho sem defeito, e seis cordeiros e um carneiro; eles serão sem defeito.
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da ’yan raguna, da kuma ’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
7 E ele preparará uma oferta de alimento, um efa por novilho, e um efa por carneiro, e pelos cordeiros, de acordo com o que sua mão conseguir, e um him de azeite por efa.
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
8 E, quando o príncipe entrar, ele entrará pelo caminho do alpendre daquele portão, e sairá pelo seu caminho.
9 “ ‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
9 Mas, quando o povo da terra vier diante do SENHOR nas festas solenes, aquele que entrar pelo caminho do portão do norte, para adorar, sairá pelo caminho do portão do sul; e aquele que entrar pelo caminho do portão do sul sairá pelo caminho do portão do norte; ele não retornará pelo caminho do portão por onde entrou, mas sairá defronte dele.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
10 E o príncipe, no meio deles, quando eles entrarem, entrará, e quando eles saírem, sairão.
11 “ ‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma ’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
11 E nas festas e nas solenidades a oferta de alimento será de um efa para o novilho, e um efa para o carneiro, e para os cordeiros o quanto ele for capaz de dar; e um him de azeite para um efa.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
12 Ora, quando o príncipe preparar uma oferta queimada voluntária, ou ofertas de paz voluntariamente ao SENHOR, alguém então lhe abrirá o portão que olha em direção ao leste, e ele preparará a oferta queimada e suas ofertas de paz, como ele fez no dia do shabat; então ele sairá, e depois de sua saída alguém fechará o portão.
13 “ ‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
13 E tu prepararás diariamente uma oferta queimada ao SENHOR de um cordeiro do primeiro ano sem defeito; tu o prepararás toda manhã.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
14 E tu prepararás uma oferta de alimento toda manhã, a sexta parte de um efa e a terça parte de um him de azeite, para temperar com fina farinha; uma oferta de alimento contínuo pela ordenança perpétua ao SENHOR.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
15 Assim, eles prepararão o cordeiro, e a oferta de alimento, e o azeite, toda manhã, para uma oferta queimada contínua.
16 “ ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin ’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
16 Assim diz o Senhor DEUS: Se o príncipe der um presente a algum de seus filhos, a sua herança será de seus filhos; será a possessão deles por herança.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar ’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na ’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
17 Mas se ele der um presente da sua herança a um dos seus servos, então isto será dele até o ano da liberdade; depois, retornará ao príncipe; mas a sua herança será de seus filhos por eles.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa ’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’ ”
18 Além disso, o príncipe não tomará da herança do povo por opressão, para empurrá-los para fora de sua possessão, mas ele dará a seus filhos a herança de sua própria possessão, para que meu povo não seja espalhado, cada homem de sua possessão.
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
19 Depois ele me levou através da entrada que estava ao lado do portão, para dentro das câmaras santas dos sacerdotes, que olhavam em direção ao norte; e eis que ali havia um lugar nos dois lados em direção ao oeste.
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
20 Então, ele me disse: Este é o lugar onde os sacerdotes ferverão a oferta pela transgressão, e a oferta pelo pecado, e onde assarão a oferta de alimentos, para que eles não as carreguem para o átrio exterior para santificarem o povo.
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
21 Então, ele me trouxe para fora, para o átrio exterior, e me fez passar pelos quatro cantos do átrio; e eis que em cada canto do átrio havia um átrio.
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
22 Nos quatro cantos do átrio havia outros átrios juntos, de quarenta côvados de comprimento e de trinta de largura; estes quatro cantos eram de uma medida.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
23 E havia uma fileira de construção ao redor deles, ao redor dos quatro; e era feita de lugares de ferver debaixo das fileiras ao redor.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
24 Então, ele me disse: Estes são os lugares daqueles que fervem, onde os ministros da casa ferverão o sacrifício do povo.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Ezequiel 46, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.