Ezequiel 35
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
1 Ademais, a palavra do SENHOR veio a mim, dizendo:
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
2 Filho do homem, posiciona a tua face contra o monte Seir, e profetiza contra ele.
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
3 E dize-lhe: Assim diz o Senhor DEUS: Eis que, ó monte Seir, eu estou contra ti, e estenderei a minha mão contra ti, e te farei extremamente assolado.
4 Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
4 Eu assolarei as tuas cidades, e tu ficarás assolado, e saberás que eu sou o SENHOR.
5 “ ‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
5 Porque tu tiveste um ódio perpétuo, e derramaste o sangue dos filhos de Israel pela força da espada no tempo da sua calamidade, e no tempo em que a sua iniquidade teve um fim;
6 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
6 portanto, como eu vivo, diz o Senhor DEUS, preparar-te-ei para o sangue, e o sangue te perseguirá; visto que tu não odiaste o sangue, o sangue te perseguirá.
7 Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
7 Assim, farei do monte Seir extremamente assolado, e cortarei fora dele aquele que passar por ele e aquele que retornar.
8 Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
8 E encherei os seus montes dos seus homens mortos; nas tuas colinas, e nos teus vales, e em todos os teus rios, eles cairão mortos pela espada.
9 Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
9 Farei de ti perpétuas assolações, e as tuas cidades não retornarão, e sabereis que eu sou o SENHOR.
10 “ ‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
10 Porquanto tu disseste: Essas duas nações, e essas duas terras serão minhas, e nós as possuiremos, considerando que o SENHOR estava ali;
11 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
11 portanto, como eu vivo, diz o Senhor DEUS, procederei conforme a tua ira, de acordo com a tua inveja que usaste do teu ódio contra eles; e me farei conhecido entre eles, quando eu tiver te julgado.
12 Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
12 E tu saberás que eu sou o SENHOR, e que eu ouvi todas as tuas blasfêmias, que falaste contra os montes de Israel, dizendo: Eles estão assolados, nos são dados para serem consumidos.
13 Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
13 Assim, com a sua boca vos vangloriastes contra mim, e multiplicastes vossas palavras contra mim. Eu as ouvi.
14 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
14 Assim diz o Senhor DEUS: Quando toda a terra se regozijar, eu farei de ti uma desolação.
15 Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’ ”
15 Como te regozijaste com a herança da casa de Israel, porque foi assolada, assim farei a ti: serás assolado, ó monte Seir, e todo o Edom, todo ele; e saberão que eu sou o SENHOR.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Ezequiel 35, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.