Deuteronômio 6

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVT

Sair da comparação
NVT Nova Versão Transformadora
1 Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
1 “Estes são os mandamentos, os decretos e os estatutos que o S enhor , seu Deus, me encarregou de lhes ensinar. Não deixem de cumpri-los na terra que em breve vocês possuirão.
2 saboda ku, ’ya’yanku, da kuma ’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
2 Vocês, seus filhos e netos temerão o S enhor , seu Deus, enquanto viverem. Se obedecerem a todos os seus decretos e mandamentos, desfrutarão de vida longa.
3 Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
3 Ouça com atenção, Israel, e tenha o cuidado de obedecer. Então tudo irá bem com vocês e terão muitos filhos na terra que produz leite e mel com fartura, exatamente como lhes prometeu o S enhor , o Deus de seus antepassados.
4 Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
4 “Ouça, ó Israel! O S enhor , nosso Deus, o S enhor é único!
5 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
5 Ame o S enhor , seu Deus, de todo o seu coração, de toda a sua alma e de toda a sua força.
6 Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
6 Guarde sempre no coração as palavras que hoje eu lhe dou.
7 Ku koya wa ’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
7 Repita-as com frequência a seus filhos. Converse a respeito delas quando estiver em casa e quando estiver caminhando, quando se deitar e quando se levantar.
8 Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
8 Amarre-as às mãos e prenda-as à testa como lembrança.
9 Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
9 Escreva-as nos batentes das portas de sua casa e em seus portões.
10 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
10 “Em breve, o S enhor , seu Deus, os conduzirá à terra que ele jurou dar a seus antepassados Abraão, Isaque e Jacó. É uma terra com cidades grandes e prósperas que vocês não construíram.
11 gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
11 As casas estarão cheias de bens que vocês não produziram. Vocês tirarão água de cisternas que não cavaram, e comerão os frutos de vinhedos e oliveiras que não plantaram. Quando tiverem comido até se fartarem nessa terra,
12 ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
12 cuidem para não se esquecerem do S enhor , que os libertou da escravidão na terra do Egito.
13 Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
13 Temam o S enhor , seu Deus, e sirvam a ele. Quando fizerem um juramento, jurem somente pelo nome dele.
14 Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
14 “Não sigam nenhum dos deuses das nações vizinhas,
15 gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
15 pois o S enhor , seu Deus, que vive entre vocês, é Deus zeloso. Se o fizerem, a ira do S enhor , seu Deus, se acenderá contra vocês, e ele os eliminará da face da terra.
16 Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
16 Não ponham à prova o S enhor , seu Deus, como fizeram quando se queixaram em Massá.
17 Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
17 Obedeçam cuidadosamente aos mandamentos do S enhor , seu Deus, bem como a todos os preceitos e decretos que ele lhes ordenou.
18 Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
18 Façam o que é certo e bom aos olhos do S enhor , para que tudo vá bem com vocês e tomem posse da boa terra em que vão entrar, a terra que o S enhor prometeu sob juramento a seus antepassados.
19 Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
19 Vocês expulsarão todos os inimigos que vivem nela, como o S enhor disse que fariam.
20 Nan gaba, sa’ad da ’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
20 “No futuro, seus filhos lhes perguntarão: ‘O que significam estes preceitos, decretos e estatutos que o S enhor , nosso Deus, lhes deu?’.
21 Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
21 “Então vocês lhes dirão: ‘Éramos escravos do faraó no Egito, mas o S enhor nos tirou de lá com sua mão forte.
22 A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
22 O S enhor realizou sinais e maravilhas diante de nossos olhos e enviou castigos terríveis sobre o Egito, o faraó e todo o seu povo.
23 Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
23 Ele nos tirou do Egito para nos dar esta terra que ele havia prometido sob juramento a nossos antepassados.
24 Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
24 E o S enhor ordenou que cumpramos todos estes decretos e temamos o S enhor , nosso Deus, para que ele sempre nos abençoe e preserve nossa vida, como tem feito até hoje.
25 In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”
25 Pois a nossa justiça estará em obedecermos cuidadosamente aos mandamentos que o S enhor , nosso Deus, nos ordenou’.”

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Deuteronômio 6, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.