Deuteronômio 31

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Sai Musa ya fita ya kuma faɗa waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila cewa,
1 E Moisés foi e falou estas palavras a todo Israel.
2 “Yanzu shekaruna ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji ya ce mini, ‘Ba za ka haye Urdun ba.’
2 E lhes disse: Hoje eu tenho cento e vinte anos de idade; não posso mais sair e entrar; também o ­SENHOR me disse: Não passarás este Jordão.
3 Ubangiji Allahnku kansa zai haye a gabanku. Zai hallaka waɗannan al’ummai da suke gabanku, za ku kuwa mallaki ƙasarsu. Yoshuwa shi ma zai haye a gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
3 O ­SENHOR teu Deus irá diante de ti, e ele destruirá estas nações de diante de ti, e tu as possuirás; e Josué irá adiante de ti, como o ­SENHOR disse.
4 Ubangiji zai yi da su, yadda ya yi da Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, waɗanda ya hallaka tare da ƙasarsu.
4 E o ­SENHOR fará a eles o que fez a Seom e a Ogue, reis dos amorreus, e à terra deles, que ele destruiu.
5 Ubangiji zai bashe su gare ku, dole kuma ku yi musu dukan abin da na umarce ku.
5 E o ­SENHOR os entregará diante da tua face, para que façais a eles conforme todos os mandamentos que eu vos dei.
6 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, ba zai taɓa barinku ko yă yashe ku ba.”
6 Sede fortes, e de boa coragem, não temais, nem vos amedronteis com eles; porque o ­SENHOR teu Deus é quem vai contigo; ele não te deixará, nem te desamparará.
7 Sai Musa ya kira Yoshuwa, ya ce masa a gaban dukan Isra’ila, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama dole ka tafi tare da mutanen nan zuwa cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse cewa za ba wa kakanninku, dole kuma ka raba ta gare su ta zama gādonsu.
7 E Moisés chamou Josué, e lhe disse diante de todo Israel: Sê forte e de boa coragem, pois deves ir com este povo à terra que o ­SENHOR jurou a seus pais, que lhes daria; e tu os farás herdá-la.
8 Ubangiji kansa yana tafe a gabanka, zai kuma kasance tare da kai, ba zai taɓa barinka ko yă yashe ka ba. Kada ka ji tsoro; kada kuma ka karai.”
8 E o ­SENHOR é quem vai diante de ti; ele estará contigo, não te deixará, nem te desamparará; não temas, nem desanimes.
9 Sai Musa ya rubuta wannan doka ya kuma ba da ita ga firistoci, ’ya’yan Lawi maza, waɗanda sukan ɗauka akwatin alkawarin Ubangiji, da kuma dukan dattawan Isra’ila.
9 E Moisés escreveu esta lei, e a entregou aos sacerdotes, os filhos de Levi, que levavam a arca do pacto do ­SENHOR, e a todos os anciãos de Israel.
10 Sa’an nan Musa ya umarce su ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a shekara ta yafe basusuwa, a lokacin Bikin Tabanakul,
10 E Moisés lhes ordenou, dizendo: Ao fim de cada sete anos, na solenidade do ano de remissão, na festa dos tabernáculos,
11 sa’ad da dukan Isra’ila suka zo, don su bayyana a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa, za ku karanta wannan doka a gabansu, a kunnuwansu.
11 quando todo Israel deverá comparecer diante do ­SENHOR teu Deus, no lugar que ele escolher, lerás esta lei diante de todo Israel aos seus ouvidos.
12 Ku tattara mutane, maza, mata da kuma yara, da baƙin da suke zama a cikin garuruwanku, saboda su saurara, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su lura, su bi dukan kalmomin wannan doka.
12 Congrega o povo, os homens, e as mulheres, e as crianças, e os estrangeiros que estão dentro de tuas portas, para que possam ouvir, e para que possam aprender, e temer ao ­SENHOR vosso Deus, e observar e cumprir todas as palavras desta lei;
13 ’Ya’yansu, waɗanda ba su san wannan doka ba, dole su ji ta, su kuma koyi tsoron Ubangiji Allahnku muddin ranku a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
13 e para que seus filhos, que não conhecerem nada desta lei, possam ouvir e aprender a temer ao ­SENHOR vosso Deus, enquanto viverdes na terra à qual ides, passando o Jordão, para possuí-la.
14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Yanzu ranar mutuwarka ta yi kusa. Ka kira Yoshuwa, ku shigo Tentin Sujada, inda zan ba shi ragamar aiki.” Saboda haka Musa da Yoshuwa suka zo, suka kuma shiga Tentin Sujada.
14 E o ­SENHOR disse a Moisés: Eis que são chegados os teus dias, para que morras; chama a Josué, e apresentai-vos no tabernáculo da congregação, para que eu possa lhe dar uma ordem. E Moisés e Josué foram, e se apresentaram no tabernáculo da congregação.
15 Ubangiji kuwa ya bayyana a Tentin Sujada a cikin ginshiƙin girgije, sai girgijen ya tsaya a ƙofar Tentin Sujada.
15 E o ­SENHOR apareceu no tabernáculo, em uma coluna de nuvem, e a coluna de nuvem ficou sobre a porta do tabernáculo.
16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Za ka huta tare da kakanninka, waɗannan mutane kuwa ba da daɗewa ba za su yi karuwanci ga baƙin alloli na ƙasar da za su shiga. Za su yashe ni su kuma karya alkawarin da na yi da su.
16 E o ­SENHOR disse a Moisés: Eis que, dormirás com teus pais; e este povo se levantará, e se prostituirá seguindo os deuses dos estrangeiros da terra, para onde irão para estar entre eles, e me abandonarão, e romperão o meu pacto que fiz com eles.
17 A wannan rana zan yi fushi da su, in kuma yashe su; zan ɓoye fuskata daga gare su, za a kuwa hallaka su. Masifu masu yawa da wahaloli masu yawa za su auka musu, a wannan rana kuwa za su ce, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu’
17 Então nesse dia a minha ira se acenderá contra ele, e os abandonarei, e esconderei deles a minha face, e eles serão devorados, e muitos males e problemas lhes acontecerão; e dirão naquele dia: Não nos alcançaram estes males porque o nosso Deus não está entre nós?
18 Tabbatacce kuwa, zan ɓoye musu fuskata saboda muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka.
18 E certamente ocultarei a minha face naquele dia, por todos os males que eles tiverem feito, porque se voltaram a outros deuses.
19 “To, sai ka rubuta wannan waƙa domin kanka, ka koya wa Isra’ilawa, ka kuma sa su rera ta, don tă zama shaida a kansu.
19 Agora, portanto, escrevei este cântico para vós, e ensinai-o aos filhos de Israel; ponde-o em suas bocas, para que este cântico me possa ser um testemunho contra os filhos de Israel.
20 Sa’ad da na kawo su cikin ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa ga kakanninsu, sa’ad da kuma suka ci suka ƙoshi, suka kuma yi ƙiba, za su juya ga waɗansu alloli su bauta musu, su ƙi ni, su kuma karya alkawarina.
20 Pois quando eu os tiver trazido à terra que jurei aos seus pais, que mana leite e mel, e quando tiverem comido e se saciado, e engordado, então eles se voltarão a outros deuses, e os servirão, e me provocarão, e romperão o meu pacto.
21 Sa’ad da kuma masifu masu yawa da wahaloli masu yawa suka auko musu, wannan waƙa za tă zama shaida a kansu, domin zuriyarsu ba za tă manta da ita ba. Na san abin da za su iya yi, kafin ma in kawo su cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa.”
21 E acontecerá que, quando lhes vierem muitos males e problemas, que este cântico testemunhará contra eles, como uma testemunha; porque ele não será esquecido nas bocas de sua semente; pois conheço a sua imaginação, o que eles fazem mesmo agora, antes que eu os tenha colocado na terra que jurei.
22 Sai Musa ya rubuta wannan waƙa a wannan rana, ya kuma koya wa Isra’ilawa.
22 Portanto, Moisés escreveu este cântico, no mesmo dia, e o ensinou aos filhos de Israel.
23 Ubangiji ya ba wa Yoshuwa ɗan Nun wannan umarni, “Ka ƙarfafa, ka kuma yi ƙarfin hali, gama za ka kawo Isra’ilawa cikin ƙasar da na yi musu alkawari da rantsuwa, ni kaina kuwa zan kasance tare da kai.”
23 E deu uma ordem a Josué, filho de Num, e disse: Sê forte e de boa coragem, porque trarás os filhos de Israel à terra que jurei a eles, e eu serei contigo.
24 Bayan Musa ya gama rubuta kalmomin dokan nan a littafi daga farko zuwa ƙarshe,
24 E aconteceu que, quando Moisés terminou de escrever as palavras desta lei em um livro, até finalizá-las.
25 sai ya ba wa Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji wannan umarni,
25 Moisés ordenou aos levitas, que levavam a arca do pacto do ­SENHOR, dizendo:
26 “Ku ɗauki wannan Littafin Doka ku sa shi kusa da akwatin alkawarin Ubangiji Allahnku. A can zai kasance a matsayin shaida a kanku.
26 Tomai este livro da lei e ponde-o ao lado da arca do pacto do ­SENHOR vosso Deus, para que ali esteja por testemunha contra ti.
27 Gama na sani yadda kuke ’yan tawaye da masu taurinkai. In kuna yin tawaye ga Ubangiji tun ina da rai tare da ku, yaya tawayen da za ku yi masa bayan na rasu!
27 Porque eu conheço a tua rebelião, e a tua arrogância; eis que, vivendo eu ainda hoje convosco, fostes rebeldes contra o ­SENHOR; e quanto mais, depois da minha morte?
28 Ku tattara dukan dattawan kabilanku, da kuma dukan hafsoshinku a gabana, saboda in faɗa waɗannan kalmomi a kunnuwansu, in kuma kira ga sama da ƙasa su zama shaida a kansu.
28 Congregai-me todos os anciãos de vossas tribos, e os vossos oficiais, para que eu possa falar estas palavras aos seus ouvidos, e chamar céus e terra para que façam registro contra eles.
29 Gama na san cewa bayan rasuwata, tabbatacce za ku lalace gaba ɗaya, ku juye daga hanyar da na umarce ku. A kwanaki masu zuwa, masifa za tă auka muku saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, ku tsokane shi har yă yi fushi ta wurin abin da hannuwanku suka yi.”
29 Porque sei que depois da minha morte, vos corrompereis completamente, e vos afastareis do caminho que vos ordenei; e nos últimos dias o mal vos virá; porque fareis mal aos olhos do ­SENHOR, para provocá-lo à ira, pela obra das vossas mãos.
30 Sai Musa ya karanta kalmomin waƙar daga farko zuwa ƙarshe a kunnuwan dukan taron jama’ar Isra’ila.
30 E Moisés falou aos ouvidos de toda a congregação de Israel as palavras deste cântico, até que se acabaram.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Deuteronômio 31, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.