Deuteronômio 27

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs ARA

Sair da comparação
ARA Almeida Revista e Atualizada 1993
1 Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
1 Moisés e os anciãos de Israel deram ordem ao povo, dizendo: Guarda todos estes mandamentos que, hoje, te ordeno.
2 Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
2 No dia em que passares o Jordão à terra que te der o Senhor , teu Deus, levantar-te-ás pedras grandes e as caiarás.
3 Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
3 Havendo-o passado, escreverás, nelas, todas as palavras desta lei, para entrares na terra que te dá o Senhor , teu Deus, terra que mana leite e mel, como te prometeu o Senhor , Deus de teus pais.
4 Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
4 Quando houveres passado o Jordão, levantarás estas pedras, que hoje te ordeno, no monte Ebal, e as caiarás.
5 Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
5 Ali, edificarás um altar ao Senhor , teu Deus, altar de pedras, sobre as quais não manejarás instrumento de ferro.
6 Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
6 De pedras toscas edificarás o altar do Senhor , teu Deus; e sobre ele lhe oferecerás holocaustos.
7 Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
7 Também sacrificarás ofertas pacíficas; ali, comerás e te alegrarás perante o Senhor , teu Deus.
8 Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
8 Nestas pedras, escreverás, mui distintamente, as palavras todas desta lei.
9 Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
9 Falou mais Moisés, juntamente com os sacerdotes levitas, a todo o Israel, dizendo: Guarda silêncio e ouve, ó Israel! Hoje, vieste a ser povo do Senhor , teu Deus.
10 Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
10 Portanto, obedecerás à voz do Senhor , teu Deus, e lhe cumprirás os mandamentos e os estatutos que hoje te ordeno.
11 A wannan rana Musa ya umarce mutane,
11 Moisés deu ordem, naquele dia, ao povo, dizendo:
12 Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
12 Quando houveres passado o Jordão, estarão sobre o monte Gerizim, para abençoarem o povo, estes: Simeão, Levi, Judá, Issacar, José e Benjamim.
13 Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
13 E estes, para amaldiçoar, estarão sobre o monte Ebal: Rúben, Gade, Aser, Zebulom, Dã e Naftali.
14 Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
14 Os levitas testificarão a todo o povo de Israel em alta voz e dirão:
15 “La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.”
15 Maldito o homem que fizer imagem de escultura ou de fundição, abominável ao Senhor , obra de artífice, e a puser em lugar oculto. E todo o povo responderá: Amém!
16 “La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.”
16 Maldito aquele que desprezar a seu pai ou a sua mãe. E todo o povo dirá: Amém!
17 “La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.”
17 Maldito aquele que mudar os marcos do seu próximo. E todo o povo dirá: Amém!
18 “La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.”
18 Maldito aquele que fizer o cego errar o caminho. E todo o povo dirá: Amém!
19 “La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.”
19 Maldito aquele que perverter o direito do estrangeiro, do órfão e da viúva. E todo o povo dirá: Amém!
20 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.”
20 Maldito aquele que se deitar com a madrasta, porquanto profanaria o leito de seu pai. E todo o povo dirá: Amém!
21 “La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.”
21 Maldito aquele que se ajuntar com animal. E todo o povo dirá: Amém!
22 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da ’yar’uwarsa, ’yar mahaifinsa ko ’yar mahaifiyarsa.”
22 Maldito aquele que se deitar com sua irmã, filha de seu pai ou filha de sua mãe. E todo o povo dirá: Amém!
23 “La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.”
23 Maldito aquele que se deitar com sua sogra. E todo o povo dirá: Amém!
24 “La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.”
24 Maldito aquele que ferir o seu próximo em oculto. E todo o povo dirá: Amém!
25 “La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.”
25 Maldito aquele que aceitar suborno para matar pessoa inocente. E todo o povo dirá: Amém!
26 “La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.”
26 Maldito aquele que não confirmar as palavras desta lei, não as cumprindo. E todo o povo dirá: Amém!

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Deuteronômio 27, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.