Deuteronômio 23
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NTLH
1 Duk wanda aka daƙe, ko yanke gabansa, ba zai shiga taron jama’ar Ubangiji ba.
1 Moisés disse ao povo: — Nenhum homem castrado ou que tenha o membro cortado poderá fazer parte do povo de Deus, o
2 Duk wanda aka haifa ta wurin cikin shege, har tsara ta goma, zuriyarsa ba za su shiga taron jama’ar Ubangiji ba, har zuwa tsara ta goma.
2 — Nenhum filho ilegítimo fará parte do povo do Senhor , nem ele nem os seus descendentes até dez gerações .
3 Ba mutumin Ammon, ko mutumin Mowab, ko kuwa wani zuriyarsu da zai shiga taron jama’ar Ubangiji, har tsara ta goma.
3 — Nenhum amonita ou moabita, até a décima geração, fará parte do povo de Deus, o Senhor . Eles ficarão de fora
4 Gama ba su zo sun tarye ku da burodi da ruwa a hanyarku, sa’ad da kuka fito daga Masar ba, sai ma suka yi haya Bala’am ɗan Beyor daga Fetor a Aram-Naharayim yă furta la’ana a kanku.
4 porque, quando vocês estavam saindo do Egito, eles não lhes deram comida nem água. E também porque pagaram Balaão, filho de Beor, da cidade de Petor, na Mesopotâmia, para amaldiçoar vocês.
5 Amma Ubangiji Allahnku bai saurari Bala’am ba, sai ya mai da la’anar ta koma albarka gare ku, domin Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku.
5 Mas o Senhor , nosso Deus, não atendeu o pedido de Balaão; pelo contrário, Deus virou a maldição em bênção porque ama vocês.
6 Kada ku yi yarjejjeniyar abuta da su, muddin kuna da rai.
6 Nunca façam coisa alguma para o bem ou proveito desses povos.
7 Kada ku yi ƙyamar mutumin Edom, gama mutumin Edom ɗan’uwanku ne. Kada ku yi ƙyamar mutumin Masar, domin kun yi zama baƙunta a ƙasarsa.
7 — Não desprezem os edomitas, pois eles são seus parentes ; nem desprezem os egípcios, pois vocês viveram como estrangeiros na terra deles.
8 ’Ya’yan da aka haifa musu na tsara ta uku za su iya shiga taron jama’ar Ubangiji.
8 Dos netos em diante, os descendentes dos edomitas e dos egípcios que morarem na terra de vocês poderão fazer parte do povo de Deus.
9 Sa’ad da kuka yi sansani don ku yi yaƙi da abokan gābanku, ku kiyaye kanku daga duk wani abu marar tsabta.
9 — Quando estiverem acampados durante uma guerra, procurem evitar qualquer coisa que os torne impuros .
10 In ɗaya daga cikin mazanku ya ƙazantu saboda zubar da maniyyi, sai yă fita daga sansani yă zauna waje da sansani.
10 Se durante a noite alguém ficar impuro por causa da perda de esperma, sairá do acampamento de manhã.
11 Amma yayinda yamma ke gabatowa sai yă wanke kansa, da fāɗuwar rana kuwa sai yă koma cikin sansani.
11 À tarde tomará um banho e ao pôr do sol poderá voltar ao acampamento.
12 Ku keɓe wuri waje da sansani inda za ku iya zuwa don yin bayan gari.
12 — Arranjem um lugar fora do acampamento onde poderão fazer necessidade.
13 Sai ku ɗauki wani abin tona ƙasa, sa’ad da kuka yi bayan gari, sai ku tona rami, ku rufe bayan garinku.
13 Junto com as suas armas levem uma pá e, antes de fazer necessidade, cavem um buraco e depois cubram as fezes com terra.
14 Gama Ubangiji Allahnku yana zagawa a cikin sansaninku don yă tsare ku, yă kuma bashe abokan gābanku gare ku. Dole sansaninku yă kasance da tsarki, saboda kada yă ga wani abu marar kyau a cikinku, har yă juya daga gare ku.
14 — O Senhor , nosso Deus, está presente no acampamento com vocês, para protegê-los e para fazer com que vocês derrotem os inimigos. Portanto, conservem o acampamento puro a fim de que Deus não encontre nele nenhuma coisa que o ofenda, para que ele não os abandone e vá embora.
15 In bawa ya tsere zuwa wurinku don mafaka, kada ku miƙa shi ga ubangidansa.
15 — Se um escravo fugir do dono e vier pedir que você lhe dê proteção, não o entregue ao dono.
16 Ku bar shi yă zauna a cikinku a duk inda yake so, da kuma a kowane garin da ya zaɓa. Kada ku tsananta masa.
16 Ele deverá ficar morando em qualquer cidade israelita que quiser e não poderá ser maltratado.
17 Kada mutumin Isra’ila ko mutuniyar Isra’ila yă zama karuwar haikali.
17 — Nenhum israelita, mulher ou homem, praticará a prostituição nos templos pagãos .
18 Kada ku kawo kuɗin a cikin gida Ubangiji Allahnku da aka samu ta wurin karuwanci wanda mace ko namiji ya yi don biyan wani alkawari, domin Ubangiji Allahnku yana ƙyamar su duka.
18 O dinheiro ganho desse modo não poderá ser levado ao Templo do Senhor para pagamento de uma promessa feita ao Senhor , nosso Deus. Deus detesta esse dinheiro.
19 Kada ku nemi ɗan’uwanku yă biya bashin da kuka ba shi da ruwa, ko kuɗi, ko abinci, ko kowane irin abin da yana iya ba da ruwa.
19 — Não cobrem juros quando emprestarem dinheiro, comida ou qualquer outra coisa a um israelita.
20 Za ku iya nemi ruwa a bashin da kuka ba baƙo, amma ba ɗan’uwanku mutumin Isra’ila ba, domin Ubangiji Allahnku yă sa muku albarka a kowane abin da kuka sa hannunku a kai, a ƙasar da kuke shiga ku ci gādonta.
20 Vocês poderão cobrar juros dos estrangeiros; mas não cobrem de outro israelita, para que o Senhor , nosso Deus, abençoe tudo o que vocês fizerem na terra que vai ser de vocês.
21 In fa kuka yi alkawari ga Ubangiji Allahnku, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama tabbatacce Ubangiji Allahnku zai neme shi daga gare ku, za ku kuma zama masu laifin zunubi.
21 — Quando você fizer uma promessa ao Senhor , nosso Deus, não demore a cumpri-la. Deus exige que a promessa seja cumprida; e é pecado deixar de fazer aquilo que você prometeu.
22 Amma in ba ku yi alkawari ba, ba kuwa zai zama muku zunubi ba.
22 Não é pecado deixar de fazer uma promessa a Deus;
23 Duk abin da ya fita daga bakinku, sai ku lura ku cika shi, kamar yadda kuka yarda da kanku, kuka yi alkawarin ga Ubangiji Allahnku da bakinku.
23 mas, se você, por vontade própria, fizer uma promessa, então deverá cumpri-la sem falta.
24 In kun shiga gonar inabin maƙwabcinku, za ku iya cin inabin da kuke so, amma kada ku sa wani a kwandonku.
24 — Quando estiver andando num caminho que atravessa a plantação de uvas de outro israelita, você poderá comer todas as uvas que quiser, porém não carregue uvas num cesto.
25 In kun shiga gonar hatsin maƙwabcinku, za ku iya murmure tsabar da hannuwanku, amma kada ku sa lauje ku yanka hatsinsa da yake tsaye.
25 E, quando estiver atravessando o campo de trigo ou de cevada que pertence a outro israelita, você poderá comer todas as espigas que puder colher com as mãos; porém não use uma foice para colher as espigas.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Deuteronômio 23, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.