Deuteronômio 1

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
1 Estas são as palavras que Moisés falou a todo Israel, deste lado do Jordão, no deserto, na planície diante do mar Vermelho, entre Parã e Tofel, e Labã, e Hazerote, e Di-Zaabe
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
2 (Há onze dias de jornada desde Horebe pelo caminho do monte Seir até Cades-Barneia).
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
3 E sucedeu que, no quadragésimo ano, no undécimo mês, no primeiro dia do mês, que Moisés falou aos filhos de Israel, conforme tudo o que o ­SENHOR lhe havia dito que ordenasse a eles;
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
4 depois que havia ferido a Seom, rei dos amorreus, que habitava em Hesbom, e a Ogue, rei de Basã, que habitava em Astarote, em Edrei,
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
5 deste lado do Jordão, na terra de Moabe, começou Moisés a declarar esta lei, dizendo:
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
6 O ­SENHOR nosso Deus nos falou em Horebe, dizendo: Haveis habitado neste monte tempo suficiente;
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
7 voltai-vos e empreendei vossa jornada, e ide ao monte dos amorreus, e a todos os lugares próximos, pela planície, pelas colinas, e pelo vale, e pelo sul, e pela beira-mar, à terra dos cananeus, e ao Líbano, ao grande rio, o rio Eufrates.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
8 Eis que coloquei a terra diante de vós; ide e possuí a terra que o ­SENHOR jurou a vossos pais, Abraão, Isaque e Jacó, que daria a eles e à sua semente depois deles.
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
9 E eu vos falei naquela ocasião, e disse: Não poderei levar-vos sozinho;
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
10 o ­SENHOR vosso Deus vos multiplicou e eis que sois hoje, uma multidão como as estrelas dos céus.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
11 (O ­SENHOR Deus dos vossos pais vos faça que sejais mil vezes mais do que já sois, e vos abençoe, como vos prometeu!)
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
12 Como posso sozinho suportar as vossas cargas, os vossos fardos, e as vossas contendas?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
13 Tomai homens sábios, e de entendimento, e conhecidos entre as vossas tribos, e os colocarei como líderes sobre vós.
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
14 E me respondestes, e dissestes: É bom que nós façamos o que dizes.
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
15 Assim, tomei os chefes das vossas tribos, homens sábios e conhecidos, e fiz deles cabeças sobre vós, capitães sobre milhares e capitães sobre centenas, e capitães sobre cinquenta, e capitães sobre dezenas, e oficiais entre vossas tribos.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin ’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin ’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
16 E, naquela ocasião, ordenei aos vossos juízes, dizendo: Ouvi as causas entre os vossos irmãos, e julgai com justiça entre cada homem e seu irmão, e o estrangeiro que está com ele.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
17 Não fareis diferenças entre pessoas em juízo, mas ouvireis os pequenos, bem como os grandes; não temereis a face do homem, porque o juízo é de Deus, e a causa que vos for difícil, a trareis diante de mim, e eu a ouvirei.
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
18 E vos ordenei, naquela ocasião, todas as coisas que deveríeis fazer.
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
19 E quando partimos de Horebe, passamos por todo aquele grande e terrível deserto, que vistes pelo caminho dos montes dos amorreus, como o ­SENHOR nosso Deus nos ordenou; e chegamos a Cades-Barneia.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
20 E eu vos disse: Chegastes aos montes dos amorreus, que o ­SENHOR nosso Deus nos dá.
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
21 Eis que o ­SENHOR teu Deus coloca a terra diante de ti; vai e possui-a, como o ­SENHOR Deus dos teus pais te disse; não temas, nem te desanimes.
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
22 E vos aproximastes de mim, cada um de vós, e dissestes: Enviaremos homens diante de nós, e eles espiarão a terra, e nos dirão por qual caminho devemos subir, e as cidades que iremos.
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
23 E o dizer me agradou bem, e tomei doze homens dentre vós, um de cada tribo;
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
24 e eles foram e subiram o monte, e chegaram ao vale de Escol, e o espiaram.
25 Suka ɗebi ’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
25 E eles tomaram em suas mãos o fruto da terra, e o trouxeram até nós, e nos trouxeram a palavra, e disseram: É uma terra boa a que o ­SENHOR nosso Deus nos dá.
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
26 Mesmo assim, não quisestes subir, mas vos rebelastes contra a ordem do ­SENHOR vosso Deus;
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
27 e murmurastes em vossas tendas, e dissestes: Portanto o ­SENHOR nos odeia, e nos trouxe da terra do Egito, para nos entregar nas mãos dos amorreus, para nos destruir.
28 Ina za mu? ’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’ ”
28 Para onde subiremos? Nossos irmãos desanimaram os nossos corações, dizendo: Esse povo é maior e mais alto do que nós; as cidades são grandes e muradas até os céus; além disso, vimos ali os filhos dos anaquins.
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
29 Então, eu vos disse: Não vos amedronteis, nem os temais.
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
30 O ­SENHOR vosso Deus, que vai diante de vós, pelejará por vós, conforme tudo o que fez por nós, no Egito, diante dos vossos olhos;
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
31 e no deserto, onde vistes como o ­SENHOR teu Deus vos levou, como um homem leva seu filho, por todo o caminho em que fostes, até que chegastes a este lugar.
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
32 No entanto, nisto não crestes no ­SENHOR vosso Deus,
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
33 que foi pelo caminho diante de vós, para vos achar um lugar onde pudésseis armar vossas tendas, à noite no fogo, para vos mostrar por qual caminho devíeis andar, e de dia na nuvem.
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
34 E o ­SENHOR ouviu a voz das vossas palavras, e irou-se, e jurou, dizendo:
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
35 Certamente, nenhum dos homens desta maligna geração verá a boa terra que jurei dar aos vossos pais,
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
36 exceto Calebe, filho de Jefoné; ele a verá, e a terra que pisou darei a ele e a seus filhos, porque seguiu fielmente o ­SENHOR.
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
37 o ­SENHOR também se irou comigo, por vossa causa, e disse: Tu também não entrarás lá.
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
38 Mas Josué, filho de Num, que está diante de vós, entrará lá; encoraja-o, pois ele fará com que Israel herde a terra.
39 Amma ’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
39 Além disso, vossas crianças, que dissestes que seriam uma presa, e vossos filhos, que naquele dia não tinham conhecimento entre o bem e o mal, entrarão na terra, e a eles a darei, e eles a possuirão.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
40 Mas quanto a vós, virai-vos e empreendei vossa jornada para o deserto, pelo caminho do mar Vermelho.
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
41 Então respondestes e me dissestes: Pecamos contra o ­SENHOR; subiremos e pelejaremos, conforme tudo o que o ­SENHOR nosso Deus nos ordenou. E depois que havíeis cingido cada homem as suas armas de guerra, e estivestes prestes a subir o monte.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’ ”
42 E o ­SENHOR me disse: Dize a eles: Não subais, nem pelejeis, pois eu não estou entre vós; para que não sejais feridos diante de vossos inimigos.
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
43 E eu vos falei, e não ouvistes, mas vos rebelastes contra a ordem do ­SENHOR, e subistes com arrogância o monte.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
44 E os amorreus, que habitavam naquele monte, vieram contra vós, e vos perseguiram, como fazem as abelhas, e vos destruíram em Seir até Horma.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
45 E voltastes, e chorastes diante do ­SENHOR; mas o ­SENHOR não ouviu a vossa voz, nem vos deu ouvidos.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
46 Assim, permanecestes em Cades por muitos dias, segundo os dias que estivestes ali.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Deuteronômio 1, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.