2 Reis 15

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 A shekara ta ashirin da bakwai ta mulkin Yerobowam sarkin Isra’ila, Azariya ɗan Amaziya, sarkin Yahuda ya fara mulki.
1 No vigésimo sétimo ano de Jeroboão, rei de Israel, começou Azarias, o filho de Amazias, rei de Judá, a reinar.
2 Yana da shekara goma sha shida sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu. Sunan mahaifiyarsa Yekoliya daga Urushalima.
2 Dezesseis anos de idade tinha ele quando começou a reinar; e reinou cinquenta e dois anos em Jerusalém. E o nome da sua mãe era Jecolias de Jerusalém.
3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yadda mahaifinsa Amaziya ya yi.
3 E ele fez aquilo que era reto à vista do ­SENHOR, segundo tudo o que o seu pai Amazias havia feito;
4 Amma bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane kuwa suka yi ta yin hadaya da ƙona turare a can.
4 salvo que os lugares altos não foram removidos; o povo ainda sacrificava e queimava incenso nos lugares altos.
5 Ubangiji ya sa wa sarki ciwon kuturta har mutuwarsa, ya kuma zauna a keɓe. Yotam ɗan sarki, shi ne ya gudanar da sha’anin fada, ya kuma shugabanci mutanen ƙasar.
5 E o ­SENHOR feriu o rei, de modo que ele ficou leproso até o dia da sua morte, e habitou em uma casa separada. E Jotão, o filho do rei esteve sobre a casa, julgando o povo da terra.
6 Game da sauran ayyukan mulkin Azariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
6 E o restante dos atos de Azarias, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Judá?
7 Azariya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi kusa da su a Birnin Dawuda. Yotam ɗansa, kuma ya gāje shi.
7 Assim, Azarias dormiu com os seus pais; e eles o sepultaram com os seus pais na cidade de Davi; e Jotão, o seu filho, reinou no seu lugar.
8 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Zakariya ɗan Yerobowam ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki wata shida.
8 No trigésimo oitavo ano de Azarias, rei de Judá, Zacarias, o filho de Jeroboão, reinou sobre Israel em Samaria por seis meses.
9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa ya yi. Bai bar aikata zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila suka yi ba.
9 E ele fez aquilo que era mau à vista do ­SENHOR; como os seus pais haviam feito; ele não se afastou dos pecados de Jeroboão, o filho de Nebate, que fez Israel pecar.
10 Sai Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla wa Zakariya maƙarƙashiya. Ya tasam masa a gaban jama’a, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
10 E Salum, o filho de Jabes, conspirou contra ele, e o feriu diante do povo, e o matou, e reinou no seu lugar.
11 Game da sauran ayyukan mulkin Zakariya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
11 E o restante dos atos de Zacarias, eis que estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Israel.
12 Ta haka maganar Ubangiji da ya yi wa Yehu ta cika, wadda ya ce, “Zuriyarka za tă zauna a kursiyin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
12 Esta foi a palavra do ­SENHOR, a qual ele falou a Jeú, dizendo: Os teus filhos se assentarão sobre o trono de Israel até a quarta geração. E assim sucedeu.
13 Shallum ɗan Yabesh ya zama sarki a shekara ta talatin da tara ta mulkin Uzziya sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki na wata ɗaya a Samariya.
13 Salum, o filho de Jabes, começou a reinar no ano trigésimo nono de Uzias, rei de Judá; e reinou um mês inteiro em Samaria.
14 Sa’an nan Menahem ɗan Gadi ya gangara daga Tirza ya haura zuwa Samariya. Ya tasam wa Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya kuma gāje shi.
14 Porque Menaém, o filho de Gadi, subiu de Tirza, e chegou a Samaria, e feriu Salum, o filho de Jabes, em Samaria, e o matou, e reinou no seu lugar.
15 Game da sauran ayyukan mulkin Shallum, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
15 E o restante dos atos de Salum, e a conspiração que ele fez, eis que estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Israel.
16 A lokacin nan sai Menahem ya taso daga Tirza, ya kai wa Tifsa hari da kowa wanda yake a birnin da kewayenta, don sun ƙi su buɗe ƙofofinsu. Ya kori Tifsa daga aiki, ya kuma tsattsaga cikin dukan mata masu juna biyu.
16 Então, Menaém feriu Tifsa, e todos os que nela estavam, e os seus termos desde Tirza; porque eles não a abriram para ele, por isso ele a feriu; e todas as mulheres dali que estavam grávidas ele partiu em dois pedaços.
17 A shekara ta talatin da takwas ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Menahem ɗan Gadi ya zama sarkin Isra’ila, ya yi mulki a Samariya shekara goma.
17 No trigésimo nono ano de Azarias, rei de Judá, Menaém, o filho de Gadi, começou a reinar sobre Israel, e reinou por dez anos em Samaria.
18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A duk tsawon mulkinsa, bai rabu da zunuban da Yerobowam ɗan Nebat ya sa Isra’ila suka aikata ba.
18 E ele fez aquilo que era mau à vista do ­SENHOR; ele não se afastou, em todos os seus dias, dos pecados de Jeroboão, o filho de Nebate, que fez Israel pecar.
19 Sai Ful sarkin Assuriya ya kai wa ƙasar hari, Menahem kuwa ya ba shi talenti dubu na azurfa don yă sami goyon bayansa, yă kuma ƙarfafa kahuwa mulkin.
19 E Pul, o rei da Assíria, veio contra a terra; e Menaém deu a Pul mil talentos de prata, para que a sua mão pudesse estar com ele, para confirmar o reino em sua mão.
20 Menahem ya tara kuɗin ne ta hanyar haraji a Isra’ila inda ya sa kowane attajiri ya ba da shekel hamsin don a ba sarkin Assuriya. Sa’an nan sarkin Assuriya ya janye, bai ƙara kasance a ƙasar ba.
20 E Menaém exigiu o dinheiro de Israel, a saber, de todos os homens poderosos em riqueza, de cada homem cinquenta shekels de prata, para dar ao rei da Assíria. Assim, o rei da Assíria retornou, e não permaneceu ali na terra.
21 Game da sauran ayyukan mulkin Menahem, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
21 Ora, o restante dos atos de Menaém, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Israel?
22 Menahem ya huta tare da kakanninsa. Fekahiya ɗansa kuma ya gāje shi.
22 E Menaém dormiu com os seus pais; e Pecaías, o seu filho, reinou no seu lugar.
23 A shekara ta hamsin ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Fekahiya ɗan Menahem ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekara biyu.
23 No quinquagésimo ano de Azarias, rei de Judá, Pecaías, o filho de Menaém, começou a reinar sobre Israel em Samaria, e reinou por dois anos.
24 Fekahiya ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat wanda ya sa Isra’ila ya aikata ba.
24 E ele fez aquilo que era mau à vista do ­SENHOR; ele não se afastou dos pecados de Jeroboão, o filho de Nebate, que fez Israel pecar.
25 Ɗaya daga cikin manyan fadawansa, Feka ɗan Remaliya, ya ƙulla masa maƙarƙashiya. Ɗauke da mutanen Gileyad hamsin, ya kashe Fekahiya tare da Argob da kuma Ariye a fadan sarki a Samariya. Ta haka Feka ya kashe Fekahiya ya kuma gāje shi.
25 Porém, Peca, o filho de Remalias, um capitão dele, conspirou contra ele, e o feriu em Samaria, no palácio da casa do rei, com Argobe e Arié, e com ele cinquenta homens dos gileaditas; e ele o matou, e reinou no seu lugar.
26 Game da sauran ayyukan mulkin Fekahiya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
26 Ora, o restante dos atos de Pecaías, e tudo o que ele fez, eis que estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Israel.
27 A shekara ta hamsin da biyu ta mulkin Azariya sarkin Yahuda, Feka ɗan Remaliya ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya yi mulki shekara ashirin.
27 No quinquagésimo segundo ano de Azarias, rei de Judá, Peca, o filho de Remalias, começou a reinar sobre Israel em Samaria, e reinou por vinte anos.
28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai kauce wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta yi ba.
28 E ele fez aquilo que era mau à vista do ­SENHOR; ele não se afastou dos pecados de Jeroboão, o filho de Nebate, que fez Israel pecar.
29 A zamanin Feka sarkin Isra’ila, Tiglat-Fileser sarkin Assuriya ya zo ya kama Iyon, Abel-Bet-Ma’aka, Yanowa da Kedesh da kuma Hazor. Ya kame Gileyad da Galili, haɗe da dukan ƙasar Naftali, ya kuma kwashi mutanen zuwa Assuriya.
29 Nos dias de Peca, rei de Israel, veio Tiglate-Pileser, rei da Assíria, e tomou Ijom, e Abel-Bete-Maaca, e Janoa, e Quedes, e Hazor, e Gileade, e a Galileia, toda a terra de Naftali, e levou-os cativos para a Assíria.
30 Sa’an nan Hosheya ɗan Ela ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya. Ya fāɗa masa ya kuma kashe shi, sa’an nan ya gāje shi a matsayin sarki a shekara ta shirin ta mulkin Yotam ɗan Uzziya.
30 E Oseias, o filho de Elá, fez conspiração contra Peca, o filho de Remalias, e o feriu, e o matou, e reinou em seu lugar, no vigésimo ano de Jotão, o filho de Uzias.
31 Game da sauran ayyukan mulkin Feka da duk abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
31 E o restante dos atos de Peca, e tudo o que ele fez, eis que estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Israel.
32 A shekara ta biyu ta mulkin Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila, Yotam ɗan Uzziya sarkin Yahuda ya fara mulki.
32 No segundo ano de Peca, o filho de Remalias, rei de Israel, Jotão, o filho de Uzias, rei de Judá, começou a reinar.
33 Ya zama sarki yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha, ’yar Zadok.
33 Vinte e cinco anos de idade tinha ele quando começou a reinar; e reinou dezesseis anos em Jerusalém. E o nome da sua mãe era Jerusa, a filha de Zadoque.
34 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji yadda mahaifinsa Uzziya ya yi.
34 E ele fez aquilo que era reto à vista do ­SENHOR, ele fez segundo tudo o que o seu pai Uzias tinha feito.
35 Duk da haka, bai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙona turare a can. Yotam ya sāke gina Ƙofar Bisa ta haikalin Ubangiji.
35 Todavia, os lugares altos não foram removidos; o povo ainda sacrificava e queimava incenso nos lugares altos. Ele edificou o portão mais alto da casa do ­SENHOR.
36 Game da sauran ayyukan mulkin Yotam da aikin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
36 Ora, o restante dos atos de Jotão, e tudo o que ele fez, não estão escritos no livro das Crônicas dos reis de Judá?
37 (A kwanakin nan Ubangiji ya fara aikan Rezin sarkin Aram da Feka ɗan Remaliya, su yi gāba da Yahuda.)
37 Naqueles dias o ­SENHOR começou a enviar Rezim, rei da Síria, e Peca, o filho de Remalias contra Judá.
38 Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda, birnin mahaifinsa. Ahaz ɗansa kuma ya gāje shi.
38 E Jotão dormiu com os seus pais, e foi sepultado com os seus pais na cidade de Davi. E Acaz, o seu filho, reinou em seu lugar.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 2 Reis 15, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.