2 Reis 11
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ
1 Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
1 E quando Atalia, a mãe de Acazias, viu que o seu filho estava morto, ela se levantou e destruiu toda a semente real.
2 Amma Yehosheba, ’yar Sarki Yoram, ’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin ’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
2 Porém Jeosabeate, a filha do rei Jeorão, irmã de Acazias, tomou Joás, o filho de Acazias, e o roubou dentre os filhos do rei que foram mortos; e eles o esconderam, a saber, ele e a sua ama, no quarto de Atalia, de modo que ele não foi morto.
3 Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
3 E ele esteve escondido com ela na casa do SENHOR por seis anos. E Atalia reinou sobre a terra.
4 A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
4 E no sétimo ano, Joiada mandou retirar os chefes das centúrias, com os capitães e a guarda, e os fez adentrar na casa do SENHOR, e fez com eles um pacto, e tomou deles um juramento na casa do SENHOR, e mostrou-lhes o filho do rei.
5 Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
5 E ele lhes ordenou, dizendo: Esta é a coisa que fareis: Uma terça parte de vós que entrar no shabat será sentinela de vigia da casa do rei;
6 kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan ’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
6 e uma terça parte estará junto ao portão de Sur; e uma terça parte, junto ao portão detrás da guarda; assim mantereis a vigia da casa, para que ela não seja destruída.
7 ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
7 E duas partes de todos vós que saírem no shabat, a saber, aqueles que manterão a guarda da casa do SENHOR, junto ao rei.
8 Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
8 E vós cercareis o rei em redor, cada homem com as suas armas em mão; e aquele que entrar nas fileiras, que seja morto; e estejais vós com o rei, quando ele sair e quando ele entrar.
9 Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
9 E os capitães sobre as centúrias fizeram segundo todas as coisas que Joiada, o sacerdote, ordenou; e tomaram, cada qual, os seus homens que deveriam entrar no shabat, com aqueles que deveriam sair no shabat, e vieram até Joiada, o sacerdote.
10 Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
10 E aos capitães sobre as centúrias o sacerdote entregou as lanças e os escudos do rei Davi, que estavam no templo do SENHOR.
11 Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
11 E a guarda permaneceu de pé, cada homem com as suas armas em punho, ao redor do rei, desde o canto direito do templo, até o canto esquerdo do templo, ao longo do altar e do templo.
12 Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
12 E ele retirou o filho do rei, e pôs a coroa sobre ele, deu-lhe o testemunho; e fizeram-lhe rei, e o ungiram; e bateram as palmas das mãos, e disseram: Deus salve o rei.
13 Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
13 E quando Atalia ouviu o barulho da guarda e do povo, ela veio até ao povo dentro do templo do SENHOR.
14 Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
14 E quando ela olhou, eis que o rei se colocava de pé junto a um pilar, como era o costume, e os príncipes e os trombeteiros junto ao rei, e todo o povo da terra se regozijava, e soprava trombetas; e Atalia rasgou as suas vestes, e gritava: Traição, traição.
15 Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
15 Porém, Joiada, o sacerdote, ordenou aos capitães de centúrias, os oficiais do exército, e disse a eles: Colocai-a para fora das fileiras; e àquele que a seguir, matai com a espada. Porque o sacerdote havia dito: Que ela não seja morta na casa do SENHOR.
16 Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
16 E eles puseram as mãos sobre ela; e ela andava pelo caminho da entrada dos cavalos à casa do rei, e ali a mataram.
17 Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
17 E Joiada fez um pacto entre o SENHOR, o rei e o povo, de que eles seriam o povo do SENHOR; também entre o rei e o povo.
18 Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade.
18 E todo o povo da terra entrou na casa de Baal, e a demoliu; os seus altares e as suas imagens quebraram por completo em pedaços, e mataram Matã, o sacerdote de Baal, diante dos altares. E o sacerdote indicou oficiais sobre a casa do SENHOR.
19 Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
19 E ele tomou os chefes das centúrias, e os capitães, e a guarda, e todo o povo da terra; e fizeram descer o rei da casa do SENHOR, e vieram pelo caminho do portão da guarda até a casa do rei. E ele se assentou no trono dos reis.
20 dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
20 E todo o povo da terra se regozijou, e a cidade ficou em silêncio; e mataram Atalia com a espada ao lado da casa do rei.
21 Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.
21 Sete anos de idade tinha Joás quando começou a reinar.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 2 Reis 11, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.