2 Crônicas 7
Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ
1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
1 Ora, quando Salomão terminou de orar, o fogo desceu do céu e consumiu a oferta queimada e os sacrifícios; e a glória do SENHOR encheu a casa.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
2 E os sacerdotes não conseguiam entrar na casa do SENHOR, porque a glória do SENHOR havia enchido a casa do SENHOR.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa,
3 E quando todos os filhos de Israel viram como o fogo desceu, e a glória do SENHOR sobre a casa, prostraram-se com a face em terra sobre o pavimento, e adoraram, e louvaram o SENHOR, dizendo: Pois ele é bom; porque a sua misericórdia dura para sempre.
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
4 Então, o rei e todo o povo ofereceram sacrifícios diante do SENHOR.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
5 E o rei Salomão ofereceu um sacrifício de vinte e dois mil bois, e cento e vinte mil ovelhas. Assim o rei e todo o povo dedicaram a casa de Deus.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
6 E os sacerdotes serviam nos seus ofícios; os levitas também com instrumentos de música do SENHOR, os quais o rei Davi, havia feito para louvar ao SENHOR, porque a sua misericórdia dura para sempre, quando Davi louvava pelo seu ministério; e os sacerdotes soavam trombetas diante deles, e todo o Israel estava em pé.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
7 Além disso, Salomão santificou o meio do átrio que estava diante da casa do SENHOR; pois ali ele ofereceu ofertas queimadas, e a gordura das ofertas de paz, porque o altar de bronze que Salomão havia feito não foi capaz de receber as ofertas queimadas, e as ofertas de alimento, e a gordura.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
8 Então, naquele mesmo tempo, Salomão manteve a festa por sete dias, e todo o Israel com ele, uma congregação mui grande, desde a entrada de Hamate até o rio do Egito.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
9 E no oitavo dia eles fizeram uma assembleia solene; porque mantiveram a dedicação do altar por sete dias, e a festa por sete dias.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
10 E no vigésimo terceiro dia do sétimo mês ele despediu o povo para as suas tendas, contentes e felizes de coração pela bondade que o SENHOR havia demonstrado para com Davi, e Salomão, e a seu povo Israel.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
11 Assim, Salomão terminou a casa do SENHOR, e a casa do rei; e tudo o que veio ao coração de Salomão para ser feito na casa do SENHOR, e na sua própria casa, ele prosperamente o efetuou.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce,
12 E o SENHOR apareceu a Salomão à noite, e disse-lhe: Ouvi a tua oração, e escolhi para mim este lugar para casa de sacrifício.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
13 Se eu fechar o céu para que não haja chuva, ou se eu ordenar às locustas que devorem a terra, ou se eu enviar peste no meio do povo;
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
14 se o meu povo, que é chamado pelo meu nome, se humilhar, e orar, e buscar a minha face, e voltar dos seus caminhos iníquos; então eu ouvirei do céu, e perdoarei os seus pecados, e sararei a sua terra.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
15 Agora os meus olhos serão abertos, e os meus ouvidos atentos à oração que é feita nesse lugar.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
16 Porque agora escolhi e santifiquei esta casa, para que o meu nome esteja nela para sempre; e os meus olhos e o meu coração estarão ali perpetuamente.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
17 E quanto a ti, se quiseres andar diante de mim, como o teu pai Davi andou, e fazer segundo tudo o que te tenho ordenado, e guardares os meus estatutos e os meus juízos;
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
18 então eu estabelecerei o trono do teu reino, conforme o pacto que fiz com Davi, o teu pai, dizendo: Não te faltará um homem para ser soberano em Israel.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
19 Porém, se vós vos desviardes, e abandonardes os meus estatutos e os meus mandamentos, que tenho posto diante de vós, e fores servir a outros deuses, e os adorares;
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
20 arrancai-vos-ei pelas raízes, da minha terra que lhes dei; e essa casa, a qual santifiquei para o meu nome, eu lançarei para longe dos meus olhos, e farei com que ela seja provérbio e escárnio entre todas as nações.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
21 E esta casa, que é elevada, será um espanto para cada um que passar por ela; de modo que dirão: Por que o SENHOR fez assim a esta terra, e a esta casa?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’ ”
22 E se responderá: Porque eles abandonaram o SENHOR Deus dos seus pais, que os tirou da terra do Egito, e se apegaram a outros deuses, e os adoraram, e os serviram; por isso ele trouxe sobre eles todo este mal.
Atalhos do teclado
- Capítulo anterior←
- Próximo capítulo→
- Versículo anteriork
- Próximo versículoj
- Limpar seleçãoEsc
- Esta ajuda?
Estude este capítulo no WhatsApp
Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 2 Crônicas 7, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.