1 João 5

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Kowa ya gaskata cewa Yesu shi ne Kiristi, shi haifaffe na Allah ne, kuma duk mai ƙaunar mahaifi kuwa, yakan ƙaunaci ɗansa ma.
1 Todo aquele que crê que Jesus é o Cristo, é nascido de Deus; e todo aquele que ama aquele que o gerou, também ama ao que dele foi gerado.
2 Ga yadda muka san cewa muna ƙaunar ’ya’yan Allah. Muna yin haka ta wurin ƙaunar Allah da kuma aikata umarnansa.
2 Nisto sabemos que amamos os filhos de Deus, quando amamos a Deus e guardamos os seus mandamentos.
3 Ƙaunar Allah ita ce, a yi biyayya da umarnansa. Umarnansa kuwa ba masu nauyi ba ne;
3 Porque este é o amor de Deus: que guardemos os seus mandamentos; e os seus mandamentos não são pesados.
4 domin duk haifaffe na Allah yana cin nasara a kan duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta ba mu wannan nasara a kan duniya.
4 Porque todo o que é nascido de Deus vence o mundo; e esta é a vitória que vence o mundo, a nossa fé.
5 Wa ya cin nasara a kan duniya? Sai wanda ya gaskata cewa Yesu Ɗan Allah ne.
5 Quem é o que vence o mundo, senão aquele que crê que Jesus é o Filho de Deus?
6 Ga wanda ya zo ta wurin ruwa da jini, wato, Yesu Kiristi. Bai zo ta wurin ruwa kaɗai ba, sai dai ta wurin ruwa da kuma jini. Ruhu ne kuwa yake ba da shaida, gama Ruhu shi ne gaskiya.
6 Este é aquele que veio por água e sangue, a saber, Jesus Cristo; não apenas por água, mas por água e por sangue. E o Espírito é o que testifica, porque o Espírito é a verdade.
7 Akwai shaidu uku, wato,
7 Porque três são os que dão testemunho no céu: o Pai, a Palavra, e o Espírito Santo; e estes três são um.
8 Ruhu, da ruwa, da kuma jini; waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce.
8 E três são os que testificam na terra: o Espírito, e a água, e o sangue; e estes três concordam em um.
9 Tun da yake mukan yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa.
9 Se recebemos o testemunho dos homens, o testemunho de Deus é maior; porque este é o testemunho de Deus, que ele testificou de seu Filho.
10 Duk wanda ya gaskata da Ɗan Allah, yana da shaidan nan a zuciyarsa. Duk wanda bai gaskata da Allah ba kuwa ya mai da shi maƙaryaci, domin bai gaskata shaidar da Allah ya bayar game da Ɗansa ba.
10 Aquele que crê no Filho de Deus tem em si mesmo o testemunho; aquele que não crê em Deus faz dele um mentiroso, porquanto não crê no testemunho que Deus deu de seu Filho.
11 Wannan kuwa ita ce shaidar; cewa Allah ya ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa.
11 E este é o testemunho: que Deus nos deu a vida eterna; e esta vida está em seu Filho.
12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai; wanda kuwa ba shi da Ɗan Allah, ba shi da rai.
12 Aquele que tem o Filho tem a vida; e aquele que não tem o Filho de Deus não tem a vida.
13 Ina rubuta waɗannan abubuwa gare ku, ku da kuka gaskata sunan Ɗan Allah domin ku san kuna da rai madawwami.
13 Estas coisas escrevi a vós que credes em o nome do Filho de Deus, a fim de que saibais que tendes a vida eterna, e para que creiais em o nome do Filho de Deus.
14 Wannan shi ne ƙarfin halin da muke da shi sa’ad da muke zuwa a gaban Allah, gama mun san cewa kome muka roƙa bisa ga nufinsa, yakan saurare mu.
14 E esta é a confiança que temos nele, que se pedirmos alguma coisa, conforme a sua vontade, ele nos ouve.
15 In kuwa muka san cewa yana sauraranmu, ko mene ne muka roƙa, mun sani, mun riga mun sami abin da muka roƙa daga gare shi ke nan.
15 E se sabemos que ele nos ouve, em tudo o que pedimos, sabemos que temos as petições que dele desejamos.
16 Kowa ya ga ɗan’uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yă yi masa addu’a. Ta dalilin mai addu’an nan kuwa, Allah zai ba da rai ga mai yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yakan kai ga mutuwa. Ban ce a yi addu’a domin wannan ba.
16 Se alguém vir o seu irmão pecar um pecado que não seja para morte, deverá orar, e Deus dará vida àquele cujo pecado não é para morte. Há um pecado que leva à morte, eu não digo que se deve orar por este.
17 Duk rashin adalci, zunubi ne, amma akwai waɗansu zunuban da ba sa kai ga mutuwa.
17 Toda a injustiça é pecado, e há pecado que não é para morte.
18 Mun san cewa kowane haifaffe na Allah ba ya cin gaba da yin zunubi; kasancewarsa haifaffe na Allah ita takan kāre shi, mugun kuwa ba zai iya cuce shi ba.
18 Sabemos que todo aquele que é nascido de Deus não peca; mas o que é gerado por Deus guarda-se a si mesmo, e o maligno não lhe toca.
19 Mun san cewa mu ’ya’yan Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun.
19 E nós sabemos que somos de Deus, e que todo o mundo jaz no maligno.
20 Mun san cewa Ɗan Allah ya zo duniya, ya kuma ba mu ganewa domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna cikinsa, shi da yake Allah na gaskiya wato, cikin Ɗansa Yesu Kiristi. Shi ne Allah na gaskiya da kuma rai na har abada.
20 E sabemos que o Filho de Deus veio, e nos deu um entendimento, que podemos conhecer aquele que é verdadeiro; e nós estamos naquele que é verdadeiro, ou seja, em seu Filho Jesus Cristo. Este é o verdadeiro Deus, e a vida eterna.
21 ’Ya’yana ƙaunatattu, ku yi nesa da gumaka.
21 Filhinhos, guardai-vos dos ídolos. Amém.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 João 5, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.