1 Crônicas 22

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
1 Então, Davi disse: Esta é a casa do SENHOR Deus, e este é o altar da oferta queimada por Israel.
2 Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
2 E Davi ordenou que se reunissem os estrangeiros que estavam na terra de Israel; e colocou pedreiros para talharem pedras trabalhadas para edificar a casa de Deus.
3 Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
3 E Davi preparou ferro em abundância para os cravos das folhas dos portões, e para as junções; e bronze em abundância de peso imensurável;
4 Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
4 também árvores de cedro em abundância; porque os sidônios e os de Tiro trouxeram muita madeira de cedro para Davi.
5 Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
5 E Davi disse: Salomão, o meu filho, é jovem e tenro, e a casa que está para ser edificada para o SENHOR precisa ser mui magnífica, de fama e de glória por todas as terras. Portanto, agora quero fazer a preparação para ela. Assim, Davi preparou sobejamente antes da sua morte.
6 Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
6 Depois, chamou Salomão, o seu filho, e o incumbiu de edificar uma casa para o SENHOR Deus de Israel.
7 Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
7 E Davi disse a Salomão: Filho meu, quanto a mim, esteve na minha mente edificar uma casa para o nome do SENHOR meu Deus.
8 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
8 Porém, a palavra do SENHOR veio a mim, dizendo: Tu tens derramado sangue em demasia, e tens feito grandes guerras; não edificarás uma casa para o meu nome, porque tens vertido muito sangue sobre a terra, à minha vista.
9 Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
9 Eis que te nascerá um filho, que será um homem de repouso; eu lhe darei repouso de todos os seus inimigos em redor; porque o seu nome será Salomão, e eu darei paz e quietude a Israel nos seus dias.
10 Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
10 Ele edificará uma casa para o meu nome; e será o meu filho, e eu serei o seu pai; e estabelecerei o trono do seu reino sobre Israel para sempre.
11 “Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
11 Agora, filho meu, o SENHOR seja contigo; e prospera, e edifica a casa do SENHOR teu Deus, como ele tem dito acerca de ti.
12 Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
12 Somente o SENHOR te dê sabedoria e entendimento, e te dê incumbência acerca de Israel, para que possa guardar a lei do SENHOR teu Deus.
13 Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
13 Então tu prosperarás, se atentares em cumprir os estatutos e juízos que o SENHOR incumbiu a Moisés a respeito de Israel; sê forte, e de boa coragem; não temas, nem fiques aturdido.
14 “Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
14 Agora, eis que na minha angústia preparei para a casa do SENHOR, cem mil talentos de ouro, e um milhão de talentos de prata; e bronze e ferro sem medida, porque é em abundância; também madeira e pedra tenho preparado: Pode aumentá-los.
15 Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
15 Além disso, há contigo, em abundância, talhadores e trabalhadores de pedra e madeira, e toda sorte de peritos para toda forma de trabalho.
16 zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
16 Do ouro, e da prata, e de bronze, e do ferro, não há número. Levanta, portanto, e estejas em ação, e o SENHOR esteja contigo.
17 Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
17 Davi também ordenou todos os príncipes de Israel para ajudar Salomão, o seu filho, dizendo:
18 Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
18 Não está o SENHOR vosso Deus convosco? E, não tem ele dado repouso em todos os lados? Porque ele tem dado todos os moradores da terra na minha mão; e a terra está subjugada diante do SENHOR, e diante do seu povo.
19 Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”
19 Agora, aplicai o vosso coração e a vossa alma a buscar o SENHOR vosso Deus; levantai-vos, portanto, e edificai o Santuário do SENHOR Deus, para trazer a arca do pacto do SENHOR, e os vasos sagrados de Deus, para a casa que está para ser edificada ao nome do SENHOR.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 22, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.