1 Crônicas 21

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Sai Shaiɗan ya tashi gāba da Isra’ila, ya zuga Dawuda ya ƙidaya Isra’ila.
1 E Satanás se levantou contra Israel, e incitou Davi a enumerar Israel.
2 Saboda haka Dawuda ya ce wa Yowab da shugabannin mayaƙa, “Ku tafi ku ƙidaya Isra’ilawa daga Beyersheba zuwa Dan. Ku kawo mini labarin saboda in san su nawa ne.”
2 E Davi disse a Joabe e aos governantes do povo: Ide, enumerai Israel desde Berseba até Dã; e trazei o número deles para mim, para que eu possa sabê-lo.
3 Amma Yowab ya amsa ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya mayaƙansa fiye da sau ɗari. Ranka yă daɗe sarki, dukansu ba bayin shugabana ba ne? Me ya sa ranka yă daɗe yake so yă yi haka? Me zai sa ka kawo laifi a kan Isra’ila?”
3 E Joabe respondeu: O SENHOR faça o seu povo uma centena de vezes maior do que ele é; mas, meu senhor e rei, não são todos servos do meu senhor? Por que então o meu senhor requer esta coisa? Por que será ele causa de transgressão para Israel?
4 Amma sarki ya nace a kan maganar da ya yi wa Yowab. Sai Yowab ya tashi ya tafi cikin dukan Isra’ila, ya kewaye sa’an nan ya dawo Urushalima.
4 Todavia, a palavra do rei prevaleceu contra Joabe. Pelo que Joabe partiu, e foi por todo o Israel, e voltou para Jerusalém.
5 Yowab ya ba labarin yawan mayaƙan wa Dawuda. A cikin Isra’ila akwai mutum miliyon da dubu ɗari ɗaya waɗanda za su iya riƙe takobi, haɗe da dubu ɗari huɗu da saba’in a Yahuda.
5 E Joabe deu a soma do número do povo a Davi. E todos os de Israel eram um milhão e cem mil homens que empunhavam a espada; e Judá era quatrocentos e setenta mil homens que empunhavam espada.
6 Amma Yowab bai haɗa da mutanen Lawi da na Benyamin a ƙidayar ba, domin bai ji daɗin umarnin sarki ba.
6 Porém, Levi e Benjamim ele não contou entre eles; porque a palavra do rei foi abominável para Joabe.
7 Wannan umarnin mugu ne a gaban Allah; saboda haka ya hukunta Isra’ila.
7 Isso desagradou a Deus, portanto ele feriu Israel.
8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai ta wurin yin wannan. Yanzu, na roƙe ka, ka ɗauke laifin bawanka. Na yi wauta sosai.”
8 E Davi disse a Deus: Pequei grandemente em fazer isso; mas, agora, imploro-te, remove a iniquidade do teu servo; por eu ter feito mui tolamente.
9 Sai Ubangiji ya ce wa Gad, mai duba na Dawuda,
9 E o SENHOR falou a Gade, o vidente de Davi, dizendo:
10 “Tafi ka faɗa wa Dawuda, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina ba ka abubuwa uku. Ka zaɓi ɗaya daga cikinsu don in aikata a kanka.’ ”
10 Vai e conta a Davi, dizendo: Assim diz o SENHOR: Ofereço-te três coisas, escolhe para ti uma delas, para que eu possa fazê-la a ti.
11 Saboda haka Gad ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka yi zaɓi,
11 Assim, Gade veio até Davi, e disse a ele: Assim diz o SENHOR: Escolhe para ti:
12 shekara uku na yunwa, wata uku na shan ɗibga a gaban abokan gābanka, sa’ad da za su bi suna kakkashe ku, ko kuwa kwana uku na takobin Ubangiji, ranakun annoba a cikin ƙasar, mala’ikan Ubangiji zai hallaka kowane sashe na Isra’ila.’ Yanzu sai ka yanke shawara yadda zan amsa wa wanda ya aiko ni.”
12 ou três anos de fome; ou três meses para seres destruído diante dos teus inimigos, enquanto a espada dos teus inimigos te supere; ou, ainda, três dias da espada do SENHOR; a saber, a peste na terra, e o anjo do SENHOR destruindo ao longo de toda costa de Israel. Agora, portanto, aconselha-te de qual palavra trarei de volta àquele que me enviou.
13 Dawuda ya ce wa Gad, “Na shiga uku. Bari in fāɗa a hannuwan Ubangiji, gama jinƙansa yana da girma sosai; amma kada ka bari in fāɗa a hannuwan mutane.”
13 E Davi disse a Gade: Estou em um grande aperto; que caiamos, agora, na mão do SENHOR; porque mui grandes são as suas misericórdias; mas que eu não caia na mão de homem.
14 Sai Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra’ila, mutane duba saba’in na Isra’ila suka mutu.
14 Assim, o SENHOR enviou peste sobre Israel; e ali caíram de Israel setenta mil homens.
15 Allah kuwa ya aiki mala’ika yă hallaka Urushalima. Amma yayinda mala’ikan yana gab da yin haka, sai Ubangiji ya gani ya kuma yi nadama saboda masifar, sai ya ce wa mala’ikan wanda yake hallaka mutane, “Ya isa! Janye hannunka.” Mala’ikan Ubangiji kuwa yana tsaye a masussukar Ornan mutumin Yebus.
15 E Deus enviou um anjo a Jerusalém para destruí-la; e enquanto ele a estava destruindo, o SENHOR olhou, e se arrependeu do mal, e disse ao anjo que destruía: Basta, detém agora a tua mão. E o anjo do SENHOR se pôs de pé junto à eira de Ornã, o jebuseu.
16 Sai Dawuda ya ɗaga ido ya ga mala’ikan Ubangiji tsaye tsakanin sama da duniya, da takobi a zāre a hannunsa ya miƙa a kan Urushalima. Sai Dawuda da dattawa, saye da rigunan makoki suka fāɗi rubda jiki.
16 E Davi ergueu os seus olhos, e viu o anjo do SENHOR de pé entre a terra e o céu, tendo a espada desembainhada na sua mão estendida sobre Jerusalém. Então, Davi e os anciãos de Israel, que estavam vestidos de pano de saco, caíram sobre as suas faces.
17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ba ni ba ne na umarta a ƙidaya mayaƙan? Ni ne wanda ya yi zunubin da kuma abin da ba daidai ba. Waɗannan dai tumaki ne. Me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, bari hannunka ya fāɗi a kaina da kuma iyalina, amma kada ka bar wannan annoba ya kasance a kan mutanenka.”
17 E Davi disse a Deus: Não sou eu quem ordenou que o povo fosse enumerado? Eu mesmo que pequei e fiz muito mal; mas quanto a estas ovelhas, o que elas fizeram? Que a tua mão, suplico-te, ó SENHOR meu Deus, esteja sobre mim, e sobre a casa do meu pai; mas não sobre o teu povo, para que sejam atormentados.
18 Sa’an nan mala’ikan Ubangiji ya umarci Gad yă faɗa wa Dawuda yă haura yă gina bagade wa Ubangiji a masussukar Ornan mutumin Yebus.
18 Então, o anjo do SENHOR mandou Gade dizer a Davi, que Davi deveria subir à eira de Ornã, o jebuseu, e erguer um altar ao SENHOR.
19 Saboda haka Dawuda ya haura cikin biyayya ga maganar da Allah ya yi da sunan Ubangiji.
19 E Davi subiu, diante da palavra de Gade, a qual ele falou em nome do SENHOR.
20 Yayinda Ornan yake sussukar alkama, sai ya juya ya ga mala’ika; ’ya’yansa maza guda huɗu da suke tare da shi suka ɓuya.
20 E Ornã volveu-se, e viu o anjo; e ele com seus quatro filhos se esconderam. Ora, Ornã estava joeirando trigo.
21 Sai Dawuda ya kusato, sa’ad da Ornan ya duba sai ya gan shi, ya bar masussukar ya rusuna a gaban Dawuda da fuskarsa har ƙasa.
21 E enquanto Davi vinha até Ornã, Ornã olhou e viu Davi, e saiu da eira, e se prostrou diante de Davi com a sua face no chão.
22 Dawuda ya ce wa Ornan, “Ka ba ni masussukarka saboda in gina bagade wa Ubangiji, don annobar da take kan mutane tă daina. Ka sayar mini ita a cikakken kuɗinta.”
22 Então, Davi disse a Ornã: Concede-me o lugar desta eira para que nela eu possa edificar um altar ao SENHOR; tu me concederás pelo preço cheio, para que a praga possa ser detida do povo.
23 Ornan ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa! Bari ranka yă daɗe, sarki yă yi duk abin da ya ga ya yi masa kyau. Duba, zan ba da shanu domin hadaya ta ƙonawa, da itacen sussuka, da kuma alkama domin hadaya ta gari. Zan ba da dukan wannan.”
23 E Ornã disse a Davi: Toma-a para ti, e que o meu senhor, o rei, faça aquilo que é bom aos seus olhos; eis que te dou também os bois por ofertas queimadas, e os instrumentos da eira por lenha, e o trigo por oferta de alimentos; tudo te dou.
24 Amma Sarki Dawuda ya amsa wa Ornan ya ce, “A’a, na nace zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai don Ubangiji ba, ko in miƙa hadaya ta ƙonawar da ba tă ci mini wani abu ba.”
24 E o rei Davi disse a Ornã: Não; mas, verdadeiramente, comprá-la-ei pelo preço cheio; porque não tomarei aquilo que é teu para o SENHOR, tampouco oferecerei ofertas queimadas sem custo.
25 Saboda haka Dawuda ya biya Ornan shekel ɗari shida na zinariya saboda wurin.
25 Assim, Davi deu a Ornã, pelo lugar o peso de seiscentos shekels de ouro.
26 Dawuda ya gina bagade wa Ubangiji a can ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wuta daga sama a kan bagaden hadaya ta ƙonawa.
26 E Davi edificou ali um altar ao SENHOR, e ofereceu ofertas queimadas e ofertas de paz, e clamou ao SENHOR; e ele lhe respondeu do céu com fogo sobre o altar da oferta queimada.
27 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana ga mala’ikan, ya kuma mayar da takobinsa a kube.
27 E o SENHOR ordenou ao anjo, e ele voltou a pôr a espada na sua bainha.
28 A lokacin, sa’ad da Dawuda ya ga cewa Ubangiji ya amsa masa a masussukar Ornan mutumin Yebus, sai ya miƙa hadayu a can.
28 Naquele momento, quando Davi viu que o SENHOR havia lhe respondido na eira de Ornã, o jebuseu; ofereceu ali sacrifícios.
29 Tabanakul na Ubangiji da Musa ya yi a hamada, da kuma bagaden hadaya ta ƙonawa a lokacin suna a tudun Gibeyon.
29 Porque o tabernáculo do SENHOR, o qual Moisés fez no deserto, e o altar da oferta queimada, estavam naquele tempo no lugar alto de Gibeão.
30 Amma Dawuda bai iya zuwa gabansa don yă yi tambaya ga Allah ba, gama yana jin tsoron takobin mala’ikan Ubangiji.
30 Porém, Davi não conseguiu ir diante dele para indagar a Deus; porque ele estava atemorizado por causa da espada do anjo do SENHOR.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 21, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.