1 Crônicas 18

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs BKJ

Sair da comparação
1 Ana nan sai Dawuda ya ci Filistiyawa ya kuma rinjaye su, ya ƙwace Gat da ƙauyukan kewayenta daga mulkin Filistiyawa.
1 Agora, depois disso, sucedeu que Davi feriu os filisteus, e os subjugou, e tomou Gate e as suas aldeias da mão dos filisteus.
2 Dawuda ya kuma ci Mowabawa, suka zama bayinsa suka kuma biya haraji.
2 E ele feriu Moabe; e os moabitas se tornaram servos de Davi, e trouxeram presentes.
3 Ban da haka, Dawuda ya yaƙi Hadadezer sarkin Zoba, har can Hamat, sa’ad da ya je don yă kafa mulkinsa a wajen Kogin Yuferites.
3 E Davi feriu Hadadezer, rei de Zobá, em Hamate, enquanto vinha para estabelecer o seu domínio junto ao rio Eufrates.
4 Dawuda ya kame keken yaƙinsa dubu ɗaya, da mahayan kekunan yaƙi dubu bakwai da sojojin kafa guda dubu ashirin. Ya yayyanke dukan agaran dawakansa, amma ya bar dawakai da suka isa jan kekunan yaƙi ɗari.
4 E Davi tomou dele mil carruagens, e sete mil cavaleiros, e vinte mil homens a pé; Davi também jarretou todos os cavalos das carruagens, mas reservou cem carruagens.
5 Da Arameyawan Damaskus suka zo su taimaki Hadadezer sarkin Zoba, sai Dawuda ya bugi dubu ashirin da biyunsu.
5 E quando os sírios de Damasco vieram para socorrer Hadadezer, o rei de Zobá, Davi matou, dos sírios, vinte e dois mil homens.
6 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a masarautar Arameyawan Damaskus. Arameyawan kuwa suka zama bayinsa, suka kuma kawo haraji. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
6 Então, Davi pôs guarnições na Síria de Damasco; e os sírios se tornaram servos de Davi, e trouxeram presentes. Assim, o SENHOR preservava a Davi onde quer que ele fosse.
7 Dawuda ya kwashe garkuwoyin zinariyan da shugabannin sojojin Hadadezer suke riƙe, ya kawo su Urushalima.
7 E Davi tomou os escudos de ouro que estavam sobre os servos de Hadadezer, e os trouxe para Jerusalém.
8 Daga Teba da Kun, garuruwan da suke ƙarƙashin Hadadezer, Dawuda ya kwashe tagulla da yawa sosai, wanda Solomon ya yi amfani don yă yi Tekun tagulla, ginshiƙai da kuma kayayyakin tagulla dabam-dabam.
8 De modo semelhante, de Tibate, e de Cum, cidades de Hadadezer, trouxe Davi grande quantidade de bronze, com o qual Salomão fez o mar de bronze, e as colunas e os vasos de bronze.
9 Sa’ad da Towu sarkin Hamat ya ji cewa Dawuda ya ci mayaƙan Hadadezer sarkin Zoba gaba ɗaya,
9 Ora, quando Toú, rei de Hamate, ouviu como Davi havia ferido todo o exército de Hadadezer, rei de Zobá;
10 sai ya aiki ɗansa Hadoram zuwa wurin Sarki Dawuda yă gaishe shi yă kuma yi masa barka da nasara a yaƙi a kan Hadadezer, wanda yake yaƙi da Towu. Hadoram ya kawo kowane irin kayayyakin zinariya da na azurfa da na tagulla.
10 ele enviou Hadorão, o seu filho, até o rei Davi, para lhe perguntar como estava, e para congratulá-lo, porque havia lutado contra Hadadezer, e por havê-lo ferido, (pois Hadadezer travou guerra contra Toú), e com ele toda sorte de vasos de ouro e prata e bronze.
11 Sarki Dawuda ya miƙa waɗannan kayayyakin ga Ubangiji, kamar yadda ya yi da azurfa da kuma zinariyan da ya kwaso daga dukan waɗannan al’ummai. Edom da Mowab, Ammonawa da Filistiyawa, da kuma Amalek.
11 Os quais o rei Davi também dedicou ao SENHOR, com a prata e o ouro que ele trouxe de todas estas nações; de Edom, e de Moabe, e dos filhos de Amom, e dos filisteus, e de Amaleque.
12 Abishai ɗan Zeruhiya ya bugi mutanen Edom dubu goma sha takwas a Kwarin Gishiri.
12 Além disso, Abisai, o filho de Zeruia; matou dos edomitas dezoito mil no vale do Sal.
13 Ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan mutanen Edom kuwa suka zama bayin Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara a ko’ina da ya tafi.
13 E ele pôs guarnições em Edom; e todos os edomitas se tornaram servos de Davi. Assim, o SENHOR preservava a Davi onde quer que ele fosse.
14 Dawuda ya yi mulki a bisa dukan Isra’ila, yana yin abin da yake daidai da kuma gaskiya saboda dukan mutanensa.
14 Assim, Davi reinou sobre todo o Israel; e executou juízo e justiça no meio de todo o seu povo.
15 Yowab ɗan Zeruhiya shi ne shugaban mayaƙa;
15 E Joabe, o filho de Zeruia, estava sobre o exército; e Josafá, o filho de Ailude, cronista;
16 Zadok ɗan Ahitub da Abimelek ɗan Abiyatar su ne firistoci;
16 e Zadoque, o filho de Aitube, e Abimeleque, o filho de Abiatar, foram os sacerdotes; e Savsa era escriba;
17 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ne shugaban Keretawa da Feletiyawa;
17 e Benaia, o filho de Joiada estava sobre os quereteus e peleteus; e os filhos de Davi eram chefes chegados ao rei.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 18, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.