1 Crônicas 14

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVT

Sair da comparação
NVT Nova Versão Transformadora
1 To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da ’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
1 Hirão, rei de Tiro, enviou a Davi mensageiros com madeira de cedro, pedreiros e carpinteiros, para que lhe construíssem um palácio.
2 Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
2 E Davi compreendeu que o S enhor o havia confirmado como rei sobre Israel e exaltado seu reino por causa de seu povo, Israel.
3 A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin ’ya’yan maza da mata.
3 Em Jerusalém, Davi tomou para si outras mulheres, que lhe deram mais filhos e filhas.
4 Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
4 Estes são os nomes dos filhos de Davi que nasceram em Jerusalém: Samua, Sobabe, Natã, Salomão,
5 Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
5 Ibar, Elisua, Elpalete,
6 Noga, Nefeg, Yafiya,
6 Nogá, Nefegue, Jafia,
7 Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
7 Elisama, Eliada e Elifelete.
8 Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
8 Quando os filisteus souberam que Davi tinha sido ungido rei de Israel, mobilizaram suas tropas para capturá-lo. Davi, porém, foi informado disso e saiu para enfrentá-los.
9 To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
9 Os filisteus chegaram e invadiram o vale de Refaim.
10 sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?”
10 Então Davi perguntou a Deus: “Devo sair e lutar contra os filisteus? Tu os entregarás em minhas mãos?”. O S
11 Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
11 Então Davi e seus soldados foram a Baal-Perazim e ali derrotaram os filisteus. Davi exclamou: “Por meu intermédio, Deus irrompeu no meio de meus inimigos como uma violenta inundação!”. Por isso, chamou aquele lugar de Baal-Perazim.
12 Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
12 Os filisteus haviam deixado seus ídolos ali, e Davi ordenou que fossem queimados.
13 Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
13 Pouco tempo depois, os filisteus voltaram a invadir o vale.
14 sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
14 Mais uma vez, Davi consultou a Deus. “Não os ataque pela frente”, respondeu Deus. “Em vez disso, dê a volta por trás deles e ataque-os perto dos álamos.
15 Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
15 Quando ouvir um som como de pés marchando por cima dos álamos, saia e ataque! É o sinal de que Deus vai à sua frente para derrotar o exército filisteu.”
16 Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
16 Davi fez como Deus ordenou e derrotou os filisteus por todo o caminho, desde Gibeom até Gezer.
17 Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.
17 Assim, a fama de Davi se espalhou por toda parte, e o S enhor fez que todas as nações o temessem.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 14, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.