1 Crônicas 12

Biblica® Buɗaɗɗen Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ (HAUSA) vs NVI

Sair da comparação
NVI Nova Versão Internacional
1 Waɗannan su ne mutanen da suka zo wurin Dawuda a Ziklag, yayinda aka kore shi daga gaban Shawulu ɗan Kish (suna cikin jarumawan da suka taimake shi a yaƙi;
1 Estes são os que se juntaram a Davi em Ziclague, onde se escondia de Saul, filho de Quis. Eles estavam entre os combatentes que o ajudaram na guerra;
2 suna da baka suna kuma iya harba kibiya, ko majajjawa da hannun dama ko na hagu; su ’yan’uwan Shawulu ne daga kabilar Benyamin):
2 utilizavam arco e flecha e a funda para atirar pedras tanto com a mão direita como com a esquerda; pertenciam à tribo de Benjamim e eram parentes de Saul:
3 Ahiyezer babbansu da Yowash ’ya’yan Shema’a maza daga Gibeya;
3 Aiezer, o chefe deles, e Joás, filhos de Semaá, de Gibeate; Jeziel e Pelete, filhos de Azmavete; Beraca, Jeú, de Anatote,
4 da Ishmahiya daga Gibeyon, wani jarumi a cikin Talatin nan, wanda shi ne shugaban Talatin;
4 e Ismaías, de Gibeom, um grande guerreiro do pelotão dos trinta, e chefe deles; Jeremias, Jaaziel, Joanã, Jozabade, de Gederate,
5 Eluzai, Yerimot, Beyaliya, Shemariya da Shefatiya daga Haruf;
5 Eluzai, Jeremote, Bealías, Semarias e Sefatias, de Harufe;
6 Elkana, Isshiya, Azarel, Yoyezer da Yashobeyam daga Kora;
6 os coreítas Elcana, Issias, Azareel, Joezer e Jasobeão;
7 da Yoyela da Zebadiya ’ya’yan Yeroham maza daga Gedor.
7 e Joela e Zebadias, filhos de Jeroão de Gedor.
8 Sai waɗansu mutanen Gad suka koma suna goyon bayan Dawuda suka kuma haɗa kai da shi a kagararsa a hamada. Su ƙwararrun mayaƙa ne, a shirye don yaƙi, kuma suna iya riƙe garkuwa da māshi. Fuskokinsu kamar fuskoki zakoki, kuma suna da sauri kamar bareyi a kan duwatsu.
8 Da tribo de Gade alguns aliaram-se a Davi em sua fortaleza no deserto. Eram guerreiros corajosos, prontos para o combate, e sabiam lutar com escudo e com lança. Tinham a bravura de um leão, e eram ágeis como gazelas nos montes.
9 Ezer shi ne babba,
9 Ézer era o primeiro; Obadias, o segundo; Eliabe, o terceiro;
10 Mismanna na huɗu, Irmiya na biyar,
10 Mismana, o quarto; Jeremias, o quinto;
11 Attai na shida, Eliyel na bakwai,
11 Atai, o sexto; Eliel, o sétimo;
12 Yohanan na takwas, Elzabad na tara,
12 Joanã, o oitavo; Elzabade, o nono;
13 Irmiya na goma da kuma Makbannai na goma sha ɗaya.
13 Jeremias, o décimo; e Macbanai era o décimo primeiro.
14 Waɗannan mutanen Gad shugabannin mayaƙa ne; ƙarami a cikinsu zai iya ƙara da mutum ɗari, kuma babba a cikin zai iya ƙara da dubu.
14 Todos esses de Gade eram chefes de exército; o menor valia por cem, e o maior enfrentava mil.
15 Su ne suka haye Urdun a wata na farko sa’ad da kogin ya yi ambaliya, suka kuma kori duk mai rai a kwarin, na wajen gabas da na wajen yamma.
15 Foram eles que atravessaram o Jordão no primeiro mês do ano, quando o rio transborda em todas as suas margens, e puseram em fuga todos os que moravam nos vales, a leste e a oeste.
16 Sauran mutanen Benyamin da waɗansu mutanen Yahuda su ma suka zo wurin Dawuda a kagararsa.
16 Alguns outros benjamitas e certos homens de Judá também vieram a Davi em sua fortaleza.
17 Sai Dawuda ya fita don yă tarye su, ya kuma ce musu, “In kun zo wurina da salama, don ku taimake ni, to, ina a shirye in bar ku ku haɗa kai tare da ni. Amma in kun zo don ku bashe ni ga abokan gābana sa’ad da hannuwana ba su da laifi a rikici, bari Allah na kakanninmu yă duba yă kuma shari’anta ku.”
17 Davi saiu ao encontro deles e lhes disse: "Se vocês vieram em paz, para me ajudarem, estou pronto para recebê-los. Mas, se querem trair-me e entregar-me aos meus inimigos quando minhas mãos não cometeram violência, que o Deus de nossos antepassados veja isso e julgue vocês".
18 Sai Ruhu ya sauko a kan Amasai, shugaban Talatin nan, sai ya ce,
18 Então o Espírito veio sobre Amasai, chefe do pelotão dos trinta, e ele disse: "Somos teus, ó Davi! Estamos contigo, ó filho de Jessé! Paz, paz seja contigo, e aos teus aliados, pois o teu Deus te ajudará". Davi os recebeu e os nomeou chefes de seus grupos de ataque.
19 Waɗansu mutanen Manasse suka haɗa kai da Dawuda sa’ad da ya tafi tare da Filistiyawa don yă yaƙi Shawulu (Shi da mutanensa ba su taimaki Filistiyawa ba domin bayan shawarwari, shugabanninsu suka salame shi. Sun ce, “Za mu biya da kawunanmu in ya koma ga maigidansa Shawulu.”)
19 Alguns soldados de Manassés desertaram para Davi quando ele foi com os filisteus guerrear contra Saul. Mas eles não ajudaram os filisteus, porque os seus chefes os aconselharam e os mandaram embora, dizendo: "Pagaremos com a vida, caso Davi deserte e passe para Saul, seu senhor".
20 Da Dawuda ya tafi Ziklag, waɗannan mutanen Manasse ne suka haɗa kai da shi. Adna, Yozabad, Yediyayel, Mika’ilu, Yozabad, Elihu da Zilletai, shugabannin ƙungiyoyi na dubu a cikin Manasse.
20 Estes foram os homens de Manassés que desertaram para Davi quando ele foi a Ziclague: Adna, Jozabade, Jediael, Micael, Jozabade, Eliú e Ziletai, chefes de batalhões de mil em Manassés.
21 Suka taimaki Dawuda a kan ƙungiyoyin hari, gama dukansu jarumawa ne sosai, kuma su shugabanni ne a cikin mayaƙansa.
21 Eles ajudaram Davi contra grupos de ataque, pois todos eles eram guerreiros valentes, e eram líderes no exército dele.
22 Kowace rana mutane suka riƙa zuwa don su taimaki Dawuda, sai da ya kasance da runduna mai girma, kamar mayaƙan Allah.
22 De fato, diariamente chegavam soldados para ajudar Davi, até que seu exército tornou-se tão grande como o exército de Deus.
23 Ga yawan mutanen shiryayyu don yaƙi waɗanda suka zo wurin Dawuda a Hebron don su mai da mulkin Shawulu gare shi, yadda Ubangiji ya faɗa.
23 Este é o número dos soldados armados para a guerra que vieram a Davi em Hebrom para entregar a ele o reino de Saul, conforme o Senhor tinha dito:
24 Mutanen Yahuda, masu riƙe garkuwa da māshi, su 6,800 shiryayyu don yaƙi;
24 Da tribo de Judá, 6. 800 armados para a guerra, com escudo e lança;
25 mutanen Simeyon, jarumawa shiryayyu don yaƙi, su 7,100;
25 Da tribo de Simeão, 7. 100 guerreiros prontos para o combate;
26 mutanen Lawi, su 4,600,
26 Da tribo de Levi, 4. 600,
27 haɗe da Yehohiyada, shugaban iyalin Haruna tare da mutane 3,700,
27 inclusive Joiada, líder da família de Arão, com 3. 700 homens,
28 da Zadok, matashi jarumi sosai, tare da shugabanni su 22 daga iyalinsa;
28 e Zadoque, um jovem e valente guerreiro, com 22 oficiais de sua família;
29 mutanen Benyamin, ’yan’uwan Shawulu, su 3,000, yawanci waɗanda suke biyayya ga gidan Shawulu sai lokacin;
29 Da tribo de Benjamim, parentes de Saul, 3. 000, a maioria dos quais era até então fiel à família de Saul;
30 mutanen Efraim, jarumawa, sanannu cikin gidajensu, su 20 800;
30 Da tribo de Efraim, 20. 800 soldados valentes, famosos em seus próprios clãs;
31 mutanen rabin kabilar Manasse, sanannu da sunaye suka zo suka mai da Dawuda sarki, su 18,000;
31 Da metade da tribo de Manassés, 18. 000, indicados por nome para fazerem Davi rei;
32 mutanen Issakar, masu fahimtar lokuta suka kuma san abin da ya kamata Isra’ila ya yi, manya 200, tare da danginsu a ƙarƙashin shugabancinsu;
32 Da tribo de Issacar, 200 chefes que sabiam como Israel devia agir em qualquer circunstância. Comandavam todos os seus parentes;
33 mutanen Zebulun, ƙwararru sojoji shiryayyu don yaƙi da kowane irin makami, suka zo don su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya, su 50,000;
33 Da tribo de Zebulom, 50. 000 soldados experientes, preparados para guerrear com qualquer tipo de arma, totalmente decididos a ajudar Davi;
34 mutanen Naftali su 1,000 shugabanni, tare da mutane 37,000 masu riƙe garkuwa da masu;
34 Da tribo de Naftali, 1. 000 líderes com 37. 000 homens armados de escudos e lanças;
35 mutanen Dan, shiryayyu don yaƙi, su 28,600;
35 Da tribo de Dã, 28. 600 prontos para o combate;
36 mutanen Asher, ƙwararrun sojoji shiryayyu don yaƙi, su 40,000;
36 Da tribo de Aser, 40. 000 soldados experientes, preparados para o combate;
37 kuma daga gabashin Urdun, mutanen Ruben, Gad da kuma rabin kabilar Manasse, masu kayan yaƙi iri-iri, su 120,000.
37 e do leste do Jordão, das tribos de Rúben e de Gade, e da metade da tribo de Manassés, 120. 000 completamente armados.
38 Dukan waɗannan mayaƙa ne waɗanda suka ba da kansu da yardar rai su yi hidima.
38 Todos esses eram homens de combate que se apresentaram voluntariamente para servirem nas fileiras. Foram a Hebrom totalmente decididos a fazerem de Davi rei sobre todo o Israel. E todos os outros israelitas tinham esse mesmo propósito.
39 Mutanen suka yi kwana uku a can tare da Dawuda, suna ci suna sha, gama iyalansu sun yi musu tanadi.
39 Ficaram com Davi três dias, comendo e bebendo, pois as suas famílias haviam fornecido provisões para eles.
40 Haka ma, maƙwabtansu daga nesa har Issakar, Zebulun da Naftali suka zo suka kawo abinci a kan jakuna, raƙuma, alfadarai da shanu. Akwai tanadin mai yawa na gari, kauɗar ɓaure, nonnan busassun ’ya’yan inabi, ruwan inabi, mai, shanu da tumaki. Duk an yi haka don a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra’ila.
40 Os habitantes das tribos vizinhas e também de lugares distantes como Issacar, Zebulom e Naftali, trouxeram-lhes muitas provisões em jumentos, camelos, mulas e bois: farinha, bolos de figo, bolos de uvas passas, vinho, azeite, bois e ovelhas, pois havia grande alegria em Israel.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar 1 Crônicas 12, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.