Mateus 24

Litafi Mai-tsarki (HAU_ULB) vs NAA

Sair da comparação
NAA Nova Almeida Atualizada 2017
1 Yesu ya fita daga cikin haikalin ya kama hanyar sa. Almajiran sa suka zo suna nuna masa ginin haikali.
1 Jesus saiu do templo e, enquanto caminhava, os seus discípulos se aproximaram para lhe mostrar as construções do templo.
2 Amma ya amsa masu yace, “kun ga dukkan wadannan abubuwan? Ina gaya maku gaskiya, ba ko dutse daya da za'a bari akan dan'uwansa wanda ba za'a rushe shi ba.”
2 Ele, porém, lhes disse:
3 Yayin da ya zauna a kan dutsen zaitun, almajiran sa suka zo wurin sa a boye suka ce, “me zai zama alamar zuwanka da kuma na karshen duniya?”
3 Jesus estava sentado no monte das Oliveiras quando os discípulos se aproximaram dele e, em particular, lhe pediram: — Diga-nos quando essas coisas vão acontecer e que sinal haverá da sua vinda e do fim dos tempos.
4 Yesu ya amsa yace dasu, “Ku kula kada wani yasa ku kauce.”
4 E Jesus respondeu:
5 Gama da yawa za su zo da sunana. Za su ce, “ni ne almasihu,” kuma za su sa da yawa su kauce.
5 Porque muitos virão em meu nome, dizendo: “Eu sou o Cristo”; e enganarão a muitos.
6 Za ku ji labarin yake-yake da kuma shelar yake-yake. Ku kula kar ku tsorata, domin dole abubuwan nan su faru; amma karshen dai tukunna.
6 E vocês ouvirão falar de guerras e rumores de guerras. Fiquem atentos e não se assustem, porque é necessário que isso aconteça, mas ainda não é o fim.
7 Gama al'umma zata tayarwa al'umma, kuma mulki zai tayarwa mulki. Za'a yi yunwa da girgizar kasa a wurare dabam dabam.
7 Porque nação se levantará contra nação, e reino, contra reino. Haverá fomes e terremotos em vários lugares.
8 Amma dukkan wadannan farkon ciwon haihuwa ne kawai.
8 Porém todas essas coisas são o princípio das dores.
9 Bayan haka za'a bada ku ga tsanani a kuma kashe ku. Dukkan al'ummai za su tsane ku saboda sunana.
9 — Vocês serão entregues para serem maltratados e eles os matarão. Vocês serão odiados por todas as nações por causa do meu nome.
10 Daga nan da yawa za su yi tuntube, kuma su ci amanar juna, su kuma tsani juna.
10 Nesse tempo, muitos hão de se escandalizar, trair e odiar uns aos outros.
11 Annabawan karya da yawa za su taso kuma susa da yawa su kauce.
11 Muitos falsos profetas se levantarão e enganarão a muitos.
12 Domin mugunta zata ribambanya, kaunar masu yawa zata yi sanyi.
12 E, por se multiplicar a maldade, o amor se esfriará de quase todos.
13 Amma duk wanda ya jure har karshe, zai sami ceto.
13 Aquele, porém, que ficar firme até o fim, esse será salvo.
14 Za'a yi wa'azin wannan bisharar mulkin a dukkan duniya don ya zama shaida akan dukkan al'ummai. Daganan karshen zai zo.
14 E será pregado este evangelho do Reino por todo o mundo, para testemunho a todas as nações. Então virá o fim.
15 Don haka, idan kun ga abin kyama mai lalatarwa, wanda Annabi Daniyel ya yi maganar sa, Ya tsaya a wuri mai tsarki (bari mai karatu ya fahimta),
15 — Quando, pois, vocês virem, situado no lugar santo, o abominável da desolação de que falou o profeta Daniel (quem lê entenda),
16 bari wadanda ke yahudiya su gudu zuwa kan duwatsu,
16 então os que estiverem na Judeia fujam para os montes.
17 Bari wanda yake kan bene kada ya sauko don daukar wani abu a cikin gidansa,
17 Quem estiver no terraço não desça para tirar de casa alguma coisa.
18 kuma wanda yake gona kar ya dawo gida domin daukar babbar rigarsa.
18 E quem estiver no campo não volte atrás para buscar a sua capa.
19 Amma kaito ga wadanda suke dauke da yaro, ko masu shayarwa a wannan kwanakin!
19 Ai das que estiverem grávidas e das que amamentarem naqueles dias!
20 Ku yi addu'a kada gudun ku ya zama lokacin hunturu, ko ranan asabaci.
20 Orem para que a fuga de vocês não aconteça no inverno, nem no sábado.
21 Domin za'ayi tsanani mai girma, wanda ba'a taba yin irin shi ba, tun farkon duniya har ya zuwa yau, a'a ba za ayi irin shi ba kuma.
21 Porque nesse tempo haverá grande tribulação, como nunca houve desde o princípio do mundo até agora e nunca jamais haverá.
22 In ba don an rage kwanakin ba, da ba mahalukin da zai tsira. Amma albarkacin zababbun, za a rage kwanakin.
22 Não tivessem aqueles dias sido abreviados, ninguém seria salvo; mas, por causa dos escolhidos, tais dias serão abreviados.
23 Sa'annan idan wani yace maku, duba, “ga Almasihu a nan!” ko, “ga Almasihu a can!” kar ku gaskata.
23 — Então, se alguém disser a vocês: “Olhem! Aqui está o Cristo!” ou: “Ali está ele!”, não acreditem.
24 Gama annabawan karya da almasihan karya za su zo suna nuna alamu da al'ajibai, don su yaudari masu yawa zuwa ga bata, in ya yiwuma har da zababbun.
24 Porque surgirão falsos cristos e falsos profetas, operando grandes sinais e prodígios, para enganar, se possível, os próprios eleitos.
25 Kun gani, na gaya maku kafin lokacin ya zo.
25 Eis que tenho predito isso a vocês.
26 Saboda haka, idan suka ce maku, “ga shi a jeji,” kar ku je jejin. Ko, “ga shi a can cikin kuryar daki,” kar ku gaskata.
26 Portanto, se disserem a vocês: “Eis que ele está no deserto!”, não vão lá. Ou, se disserem: “Eis que ele está no interior da casa!”, não acreditem.
27 Yadda walkiya ke haskakawa daga gabas zuwa yamma, haka nan zuwan Dan mutum zai zama.
27 Porque, assim como o relâmpago sai do Oriente e brilha até o Ocidente, assim será a vinda do Filho do Homem.
28 Duk inda mushe yake, nan ungulai suke taruwa.
28 Onde estiver o cadáver, aí se ajuntarão os abutres.
29 Amma nan da nan bayan kwanakin tsananin nan, rana za ta duhunta, wata kuma ba zai ba da haskensa ba, taurari kuma za su fado daga sama, ikokin sammai za su girgiza.
29 — Logo em seguida à tribulação daqueles dias, o sol escurecerá, a lua não dará a sua claridade, as estrelas cairão do firmamento e os poderes dos céus serão abalados.
30 Sa'annan alamar Dan Mutum za ta bayyana a sararin sama, kuma dukkan kabilun duniya za su yi bakin ciki. Za su ga Dan Mutun na zuwa a gajimarai da iko da daukaka mai girma.
30 Então aparecerá no céu o sinal do Filho do Homem. Todos os povos da terra se lamentarão e verão o Filho do Homem vindo sobre as nuvens do céu, com poder e grande glória.
31 Zai aiki mala'ikunsa, da karar kaho mai karfi, kuma za su tattara dukkan zababbu daga dukkan kusurwoyi hudu, daga karshen sararin sama har zuwa wani karshen.
31 E ele enviará os seus anjos, com grande som de trombeta, os quais reunirão os seus escolhidos dos quatro ventos, de uma a outra extremidade dos céus.
32 Kuyi koyi da itacen baure. Da zaran reshen sa ya yi toho ya fara bada ganye, za ku sani bazara ta kusa.
32 — Aprendam a parábola da figueira: quando já os seus ramos se renovam e as folhas brotam, vocês sabem que o verão está próximo.
33 Haka kuma, idan kun ga dukkan wadannan abubuwa, ya kamata ku sani, Ya yi kusa, ya na bakin kofa.
33 Assim, também vocês, quando virem todas estas coisas, saibam que está próximo, às portas.
34 Ina gaya maku gaskiya, wannan zamanin ba zai wuce ba, sai dukkan wadannan abubuwan sun faru.
34 Em verdade lhes digo que não passará esta geração sem que tudo isto aconteça.
35 Sama da kasa za su shude, amma kalmomina ba za su shude ba.
35 Passará o céu e a terra, porém as minhas palavras não passarão.
36 Amma game da ranan nan ko sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun sama, ko Dan, sai Uban kadai.
36 — Mas a respeito daquele dia e hora ninguém sabe, nem os anjos dos céus, nem o Filho, senão o Pai.
37 Kamar yadda kwanakin Nuhu suke, haka zai zama game da zuwan Dan Mutum.
37 Pois assim como foi nos dias de Noé, assim será também a vinda do Filho do Homem.
38 A wadannan kwankin kafin zuwan ruwan tsufana suna ci suna sha, suna aure suna aurarwa har ranar da Nuhu ya shiga jirgin,
38 Pois assim como nos dias anteriores ao dilúvio comiam e bebiam, casavam e davam-se em casamento, até o dia em que Noé entrou na arca,
39 ba su san kome ba har ruwan ya zo ya cinye su_ haka ma zuwan Dan Mutun zai zama.
39 e não o perceberam, até que veio o dilúvio e os levou a todos, assim será também a vinda do Filho do Homem.
40 Sa'annan mutane biyu zasu kasance a gona za a dauke daya, a bar daya a baya.
40 Então dois estarão no campo: um será levado, e o outro será deixado;
41 Mata biyu na nika a manika za a dauke daya, za a bar dayar.
41 duas mulheres estarão trabalhando num moinho: uma será levada, e a outra será deixada.
42 Don haka sai ku yi zaman tsaro, domin baku san ranar da Ubangijinku zai zo ba.
42 — Portanto, vigiem, porque vocês não sabem em que dia virá o Senhor de vocês.
43 Amma ku san wannan, idan maigida ya san lokacin da barawo zai zo, zai zauna a shirye ba zai bar gidan sa har a balle a shiga ba.
43 Porém, considerem isto: se o pai de família soubesse a que hora viria o ladrão, vigiaria e não deixaria que a sua casa fosse arrombada.
44 Don haka sai ku shirya, domin Dan Mutum zai zo a sa'ar da ba ku yi zato ba.
44 Por isso, estejam também vocês preparados, porque o Filho do Homem virá à hora em que vocês menos esperam.
45 To wanene amintaccen bawannan mai hikima, wanda maigidan sa ya sa ya kula mar da gida, domin ya ba su abinci a kan lokaci?
45 — Quem é, pois, o servo fiel e prudente, a quem o senhor deixou encarregado dos demais servos, para lhes dar o sustento a seu tempo?
46 Mai albarka ne bawan, da mai gidan zai same shi a kan aikin sa a lokacin da ya dawo.
46 Bem-aventurado aquele servo a quem seu senhor, quando vier, achar fazendo assim.
47 Ina gaya maku gaskiya mai gidan zai dora shi a kan dukkan a binda yake da shi.
47 Em verdade lhes digo que lhe confiará todos os seus bens.
48 Amma idan mugun bawa ya ce a zuciyarsa, “maigida na ya yi jinkiri,”
48 Mas o que acontecerá se aquele servo, sendo mau, disser consigo mesmo: “Meu senhor demora para vir”,
49 sai ya fara dukan sauran barorin, ya yi ta ci da sha tare da mashaya,
49 e começar a espancar os seus companheiros e a comer e beber com os bêbados?
50 uban gidan bawan zai dawo a ranar da bawan bai zata ba, a lokacin da bai sani ba.
50 Virá o senhor daquele servo, em dia em que não o espera e em hora que não sabe,
51 Uban gidansa zai datsa shi biyu, karshen sa zai zama daidai da na munafukai, za a sashi inda a ke kuka da cizon hakora.
51 e irá aplicar-lhe um castigo severo, condenando-o com os hipócritas. Ali haverá choro e ranger de dentes.

Ler em outra tradução

Comparar com outra

Estude este capítulo no WhatsApp

Peça à IA da Bíblia Fala para explicar Mateus 24, comparar traduções ou montar um estudo — tudo direto pelo WhatsApp.